• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Tarayya Ba Ta Da Hurumin Sauraran Karar Masarautar Kano – Falana

byAbubakar Sulaiman
1 year ago
Kotu

A makon nan ne dai babbar kotun tarayya da ke Kano ta ce tana da hurumin sauraren karar da aka shigar gabanta na take hakkin dan Adam da tsohon Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero da Aminu Babba Dan’agundi suka shigar. Wannan hukuncin ya biyo bayan mayar da Sarki Muhammad Sanusi II kan kujerarsa.

Kotu ta bayar da wani umarnin da ta hana Gwamna Abba Yusuf na Kano mayar da Sanusi kan mukaminsa har sai an warware wata karar da aka shigar a kan batun dawo da Sarki Sanusi. Haka kuma umurnin ya nuna adawa da soke masarautun Bichi, da Gaya, da Karaye, da kuma Rano—a karkashin wani kudiri da majalisar dokokin jihar ta zartar a baya.

  • Kwankwaso Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yin Katsa-landan A Harkokin Kano
  • Tsautsayin Sallah: An Tsinci Gawar Wata Mata A Gidan Malamin Tsibbu A Kano

Masanin shari’a Femi Falana ya bayar da hujjar cewa bisa ga sashe na 254 (C) (1) na kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999 da aka yi wa kwaskwarima, kotun masana’antu ta kasa ba ta da hurumin shari’ar sarauta.

Ya jaddada cewa, duk da cewa sarkin da aka tsige ba tare da an yi masa adalci ba yana da hakkin a yi masa shari’a, babban abin da ake da’awa a wannan shari’ar bai kamata ya dogara ne kan aiwatar da muhimman hakkokinsu ba, sai dai a kan wani batu na musamman na masarautu, wanda ya sabawa hurumin babban kotun tarayya.

Shigar da babbar kotun tarayya kan takaddamar tsige Sarki Aminu Ado Bayero da mayar da Sarki Sanusi Lamido Sanusi kan mukaminsa na kamanceceniya da wani mataki da ya ci karo da hukuncin da kotun koli ta yanke kan shari’ar Sarki Tukur da gwamnatin jihar Gongola a shekarar 1987 4 NWLR (117) 517.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)
Masarautu

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

January 12, 2025
Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)
Masarautu

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

July 31, 2024
Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa
Labarai

Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa

July 22, 2024
Next Post
Alhajin Filato Guda Ya Rasu A Makkah Bayan Jiyya

Alhajin Filato Guda Ya Rasu A Makkah Bayan Jiyya

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version