• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Tarayya Ba Ta Da Hurumin Sauraran Karar Masarautar Kano – Falana

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Masarautu
0
Kotun Tarayya Ba Ta Da Hurumin Sauraran Karar Masarautar Kano – Falana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A makon nan ne dai babbar kotun tarayya da ke Kano ta ce tana da hurumin sauraren karar da aka shigar gabanta na take hakkin dan Adam da tsohon Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero da Aminu Babba Dan’agundi suka shigar. Wannan hukuncin ya biyo bayan mayar da Sarki Muhammad Sanusi II kan kujerarsa.

Kotu ta bayar da wani umarnin da ta hana Gwamna Abba Yusuf na Kano mayar da Sanusi kan mukaminsa har sai an warware wata karar da aka shigar a kan batun dawo da Sarki Sanusi. Haka kuma umurnin ya nuna adawa da soke masarautun Bichi, da Gaya, da Karaye, da kuma Rano—a karkashin wani kudiri da majalisar dokokin jihar ta zartar a baya.

  • Kwankwaso Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yin Katsa-landan A Harkokin Kano
  • Tsautsayin Sallah: An Tsinci Gawar Wata Mata A Gidan Malamin Tsibbu A Kano

Masanin shari’a Femi Falana ya bayar da hujjar cewa bisa ga sashe na 254 (C) (1) na kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999 da aka yi wa kwaskwarima, kotun masana’antu ta kasa ba ta da hurumin shari’ar sarauta.

Ya jaddada cewa, duk da cewa sarkin da aka tsige ba tare da an yi masa adalci ba yana da hakkin a yi masa shari’a, babban abin da ake da’awa a wannan shari’ar bai kamata ya dogara ne kan aiwatar da muhimman hakkokinsu ba, sai dai a kan wani batu na musamman na masarautu, wanda ya sabawa hurumin babban kotun tarayya.

Shigar da babbar kotun tarayya kan takaddamar tsige Sarki Aminu Ado Bayero da mayar da Sarki Sanusi Lamido Sanusi kan mukaminsa na kamanceceniya da wani mataki da ya ci karo da hukuncin da kotun koli ta yanke kan shari’ar Sarki Tukur da gwamnatin jihar Gongola a shekarar 1987 4 NWLR (117) 517.

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba KabirAlh. Aminu Ado BayeroAPCkanoNNPPSunusi Lamido
ShareTweetSendShare
Previous Post

An kammala Aikin Hajjin Bana 1445/2024

Next Post

Alhajin Filato Guda Ya Rasu A Makkah Bayan Jiyya

Related

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)
Masarautu

Tarihin Daular Borno Da Sarakunanta (3)

6 months ago
Alh. Hassan Baita Ubawaru (Ma'ajin Hausawan Turai)
Masarautu

Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai

12 months ago
Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa
Labarai

Wakilin Gwale A Majalisar Kano Ya Zargi Magoya Bayan Sarki Aminu Da Cin Zarafinsa

12 months ago
Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)
Masarautu

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (2)

12 months ago
Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla
Masarautu

Rikicin Sarautar Kano: Yadda Gwamnatin Abba Ta Sauya Alkibla

12 months ago
Tinubu Zai Halarci  Zikirin Juma’a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa
Addini

Tinubu Zai Halarci Zikirin Juma’a A Fadar Aminu Ado Ta Nassarawa

1 year ago
Next Post
Alhajin Filato Guda Ya Rasu A Makkah Bayan Jiyya

Alhajin Filato Guda Ya Rasu A Makkah Bayan Jiyya

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.