Haruna Akarada">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTAUNAWA

Kowa Ya Ci Bashin Noma Sai Ya Biya – Shugaban RIFAN Na Kano   

by Haruna Akarada
January 19, 2021
in TATTAUNAWA
3 min read
Shugaban RIFAN
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban Kungiyar Manoman Shinkafa na Kasa  (RIFAN) reshen Jihar Kano, ALHAJI ABUBAKAR HARUNA ALI YAU, ya sami tattaunawa da Wakilin LEADERSHIP A YAU, HARUNA AKARADA, inda wannan tattaunawar an yi ta ne dangane da bai wa mutane basukan kayan noma, amma kuma biyan ya gagara. Wannan ya sa muka leka, domin jin irin matakan da wannan kungiyar za ta dauka. Ga dai yadda hirar ta kasance:

 

samndaads

Akwai mutanen da ku ka bai wa bashin noma da alama wasu sun ci kuma sun ki biya, wanne kira ka ke yi wa irin wannan mutane domin su dawo da abin da suka ranta?  

To gaskiya abin da zan ce shi ne mutanenmu na Arewa ba su da cika alkawari domin ba ma son biyan bashi, kuma wannan kudi mu muka je muka ciyo bashi a babban bankin kasa wato CBN, dalilin karbar wannan bashi domin mutanenmu su fita daga halin da suke ciki, amma sun karba sun yi shiru kuma shi wannan babbabn banki ya ce lallai mu dawo masa da duk kudin da muka karba.

 

Mutane masu karbar wannan bashi baka ganin cewa gani suke yi duk wanda ya ci gani yake ya ci banza saboda na gwamnati ne?

Eh, to! Koma dai me mutum za ice ya sani, kafin ka karbi wannan kaya an gaya maka bashi ne, akasarinmu duk musulmi ne kuma kowa ya san illar bashi a Musulunci saboda haka mutane suna daukar wannan abin da wasa kuma bashi ne ko bayan ranka ana binka wannan bashi. Wannan ana yi ne domin tattalin arzikin kasar nan ya karu, wannan shi ne yanzu irin wannan sace-sace da ake ta fama da shi, ita gwamnati tana yin wannan ne domin ta rage zaman banza, idan kana samun irin wannan tallafin yaushe za ka shiga irin waccan harka, ka ga ba zai yiwu ba.

 

Idan ya zamana ana karba ba’a biya, wane sakamako lamarin zai bayar?

Gaskiya abubuwa za su kara lalacewa, kuma bari na baka misali, lokacin da aka shiga cutar Korona wanda ta wuce, wannan lokacin da ba mu da abinci a kasar ai da an shiga mummunan hali kuma wannan harka shekararmu uku muna ba da wannan bashin adaidai wannan lokacin kasar ta shiga jerin kasashe masu noma shinkafa kuma ita kanta kasar a baya tana kashe makudan kudi wajen shigo da shinkafa, na wajen tiriliyan daya a duk lokaci, amma wannnan lokaci duk wannan kudi suna nan gida ba a kai su ko’ina ba. Amma mutane gani suke yi sun ci banza wallahi ba wannan maganar dole a biya.

 

Wato duk wanda ka ga mun ba wannan kaya sai ya kai mun ga gonarsa tukunna, kuma su mutananmu akwai dabara sosai, idan an toshe can sai su bude can. Ganin haka mutane duk wanda za mu ba wa wannan bashi sai an je kashi biyu, sannan za mu ba shi, kai sanda ka zo karbar wannan bashi ka zo da hotanka da BBN dinka  da lambar wayarka. To ta ina zaka gudu komai naka yana wajanmu. To an baka bashin 100,000 wani ya karba ya baka 20,000. Wannan ba daidai bane.

 

Wane mataki za a dauka domin dawo da wannan kudin kenan? 

To, za mu koma da duk wannan hotunan mutanen da suka ci wannan bashi zuwa ga hukuma domin su dawo da kudin.

SendShareTweetShare
Previous Post

Cikin Mako Biyu Sojoji Sun Kwace Sama Da Motocin ISWAP 20

Next Post

Kwamitin Tallafa Wa Marayu Na JIBWIS-FCT Ya Gudanar Da Taron Karshen Shekara

RelatedPosts

Har Yanzu Babu Sabuwar Kwalta Ko Kwalbati A Garin Giwa – Kwamred Alkurkawee

Har Yanzu Babu Sabuwar Kwalta Ko Kwalbati A Garin Giwa – Kwamred Alkurkawee

by Haruna Akarada
2 days ago
0

Daga Idris Umar Game da more romon dimukradiyya da wasu...

Zaman Lafiya

Marasa Son Tabbatuwar Zaman Lafiya A Nijeriya Ke Sukar Furucin Gwamna Bala Kan Fulani, Inji Ladan Salihu

by Haruna Akarada
6 days ago
0

DAKTA LADAN SALIHU Shi ne shugaban ma’aikatan gidan gwamnatin jihar...

Cigaba

Mun Samar Da Daftarin Cigaba Na Shekara 10 Ne Domin Kafa Harsashin Inganta Rayuwar Gombawa –Gwamna Inuwa

by Haruna Akarada
1 week ago
0

ALHAJI MUHAMMAD INUWA YAHAYA Shine gwamnan jihar Gombe, a wani hira ...

Next Post
JIBWIS-FCT

Kwamitin Tallafa Wa Marayu Na JIBWIS-FCT Ya Gudanar Da Taron Karshen Shekara

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version