Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home MANYAN LABARAI

Ku Ajiye Makamanku Nan Da Wata Biyu – Gwamnan Zamfara Ga ’Yan Bindiga

by Muhammad
March 10, 2021
in MANYAN LABARAI, Uncategorized
2 min read
Matawalle
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Hussaini Yero,

Gwamna Jihar Zamfara, Hon. Bello Muhammad Matawalle Maradun, ya ba wa ’yan bindiga masu garkuwa da mutane wa’adin wata biyu da su ajiye makamansu ko kuma su gamu da fushin jami’an tsaro.

Matawallen Maradun ya bayyana haka ne a jiya Talata da yamma lokacin da ya ke yi wa al”ummar jihar jawabi a kan matsalar tsaro da ta addabi jihar tasa.

Hon Matawalle ya bayyana cewa, bayan sako dalibai mata na sakandiren Jangebe da aka sace a ranar 26 ga Fabrairu, 2021, ya samu ganawa da Shugaban Kasa Muhammad Buhari akan lamarin.

Ya bayyana cewa, Shugaban Kasa ya sanya dokar hana zirga-zirgar jiragen sama da hakar ma’adanai ba tare da izini ba a fadin jihar ta Zamfara kuma wannan dokar nan daram, inda duk wanda ya saba ma ta, zai gamu da fushin jami’an tsaro.

Haka kazalika, Matawalle ya tabbatar da cewa, Shugaban Kasa Muhammad Buhari ya aminta da sulhu ga masu son sulhun, amma wadanda ba sa son sulhu, lallai za a tarwatsa su a duk inda suke a fadin jihar.

“Don haka muka ba wa ’yan bindiga wa”adin wata biyu da su mika makamansu da gaggawa ko kuma su gamu da fushin jami’an tsaro,” inji shi.

Gwamna Matawalle ya kuma bayyana wasu dokoki da za su fara aiki nan take, don ganin an magance matsalar tsaro a fadin Jihar, yana mai cewa, duk dan siyasa da aka samu da hannu wajen kawo matsalar matsalar tsaro zai gamu da hukunci, kuma sarakuna da shugabannin Kananan Hukumomi dole ne su zauna a garuruwansu, don sanin masu shiga da fice.

Kuma batun hawa babur mutum uku da kuma jerin gwanon mashina haramun ne a fadin Jihar ta Zamfara. Ya kara da cewa, haramcin ‘yan sa-kai da ayyukansu ya na nan daram da kuma yawo da makamai.

“Duk wanda ya ki bin wadannan dokokin, lallai zai gamu da fushin jami’an tsaro,” inji Gwamna Matawalle Maradun.

SendShareTweetShare
Previous Post

Tsaro: Shugabannin Rundunar Sojoji Sun Yi Wa Zamfara Dirar Mikiya

Next Post

Jihar Bauchi Ta Karbi Kashin Farko Na Rigakafin Korona

RelatedPosts

Gwamnatin Kaduna Ta Yi Wa Karnuka 6,250 Allurar Rigakafin Cutar Rabis

Gwamnatin Kaduna Ta Yi Wa Karnuka 6,250 Allurar Rigakafin Cutar Rabis

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Daga Bello Hamza, Abuja Gwamnatin jihar Kaduna ta samu nasarra...

Sufeton

Jan Aikin Da Ke Gaban Sabon Babban Sufeton ‘Yan Sanda

by Muhammad
4 days ago
0

Waiwaye Game Da Manyan Sufetocin Da Aka Taba Nadawa A...

Malaman

Yajin Aiki: Malaman Jami’o’i Sun Ratse, Na Kwalejojin Fasaha Sun Tsunduma  

by Muhammad
4 days ago
0

Malaman jami’o’i a karkashin kungiyarsu ta ASUU sun ratse daga...

Next Post
Jihar Bauchi Ta Karbi Kashin Farko Na Rigakafin Korona

Jihar Bauchi Ta Karbi Kashin Farko Na Rigakafin Korona

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version