• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi

by Bilkisu Tijjani and Sulaiman
1 month ago
in Uwargida Sarautar Mata
0
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban hatsarin da haihuwa ke zuwa da shi dake jawo asarar rayukan mata bayan haihuwa shi ne zubar jini bayan haihuwar wato Post Partum Hemorrhage a likitance dake faruwa. Wannan shi ne lokacin da dariya ke rikidewa ta koma kuka, wato murna ta koma ciki, daga murnar haihuwa a koma kukan mutuwa.

Sau tari wanda bai sani ba zai tunanin fitar yaro shi ne haihuwa lafiya, shi ne mafi mahimmanci. Amma wannan ba shi ne haihuwa lafiya ba. Haihuwa lafiya shi ne a ga bayan fitar yaro Mahaifa ta murda ta harba wato contracton ta yadda hakan zai sanadiyar fitowar placenta wato (mabiyiya ko abin da Hausa kance uwa ta biya). Kai wani lokacin koda uwa ta biya akwai bukatar sai mahaifa ta yi wannan harbawar. Idan ba ta harba ba hakan ba zai sa jijiyoyin jini su toshe ba don haka mace za ta ci gaba da zubar da jini, wanda wannan shike kashe mace. Wani lokacin hatsarin placenta din ce ma ke manne mahaifar ta yadda in aka jawo sai de ta taho hade da mahaifar ta tidota. Shi ya sa haihuwa tsallake siradi ce ba karami ba.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
  • Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

Toh abin da ke taimaka wa wannan harbawar shi ne ai maza-maza ai stimulating maman mace, shi ya sa wani lokacin ma in mace na nakuda akan iya bukatar a kawo yaron da take shayarwa domin ya kama maman hakan zai taimaka wajen contraction din mahaifarta, ko kuma in ba yaro a ce mijinta ya tsaya ya rika kama mamanta, in babu duk daya sai dai nurses su yi mata.

To waccan hikimar ta stimulating nipple na da matukar mahimmanci har bayan haihuwa, wannan ta sanya game kallon fina-finan likitoci na haihuwa za ku ga da an ciro yaro cikin jininsa da komai za’a dora wa uwa shi ya kama mama domin ya taimakamata ya sa mahaifarta harbawa jinin haihuwa ya tsaya, wannan ita ce hikimar fata zuwa fata, nan da nan za ku ga likitoci sun dorasa a mama saboda hatsarin daka iya biyo baya.

Haka zalika wannan jinin haihuwar duk da an fi ganin zubarsa nan da nan bayan haihuwa cikin awa 24 na yini. Haka zalika kananan ma’aikatan lafiya ku sani yana iya faruwa tun daga bayan kwana 1 da haihuwa zuwa sati 6. Matuwar macen da aka san ta haihu kasa da sati 6 ta zo asibiti da complaint na zubar jini to ku sani yana iya kasancewa Post Partum Hemorrhage har sai in kun gano wani abun daban, don haka a lura da kyau, kar a dau zubar jini matsayin ba mai tsanani ba abu ba don kurum kila an yi satuttuka da haihuwa ko kwana 3 uku.

Labarai Masu Nasaba

Ki Bar Auna Yadda Mijinki Yake Miki Da Yadda Wani Yake Wa Matarsa

Ko Kin San… Yadda Ake Magance Cutar Sanyi Ga Ma’aurata (Infection)

Haka zalika koda ba ki fuskanci matsalar zubar jini ba, ki daure ki shayar da jaririnki hakan zai ci gaba da sa mahaifarki harbawa ta taso daga mararki ta koma kasan cikinki cikin sati 2 da haihuwa, hakan zai rage miki tsananin ciwon mara duk da shayarwa akwai zafi wani lokacin.

Za Mu Ci Gaba Mako Mai Zuwa Insha Allahu

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

Next Post

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

Related

Ki Bar Auna Yadda Mijinki Yake Miki Da Yadda Wani Yake Wa Matarsa
Uwargida Sarautar Mata

Ki Bar Auna Yadda Mijinki Yake Miki Da Yadda Wani Yake Wa Matarsa

6 days ago
Ko Kin San… Yadda Ake Magance Cutar Sanyi Ga Ma’aurata (Infection)
Uwargida Sarautar Mata

Ko Kin San… Yadda Ake Magance Cutar Sanyi Ga Ma’aurata (Infection)

6 days ago
aure
Uwargida Sarautar Mata

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

2 months ago
Haihuwa
Uwargida Sarautar Mata

Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

4 months ago
Haihuwa
Uwargida Sarautar Mata

A Rungumi Hakuri A Zaman Aure ‘Yan’uwa Mata

6 months ago
aure
Uwargida Sarautar Mata

Mu Tsare Martabar Aure Don Kiyaye Makomarmu

8 months ago
Next Post
Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

LABARAI MASU NASABA

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

July 26, 2025
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

July 26, 2025
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

July 26, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.