• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kun Kasa Magana A Lokacin Buhari, Ba Ku Da Damar Sukar Tinubu – Matasan Arewa

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
2 years ago
in Labarai
0
Goron Jumu’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Matasan Arewa maso yamma ta nuna rashin dacewar kalaman kungiyar dattawan Katsina da suka bukaci Shugaba Bola Tinubu da ya canza matakan da Gwamnatinsa ta dauka ko kuma ya rasa goyon bayan yankin a zaben 2027. 

Ko’odinetan kungiyar, Alhaji Murtala Aliyu Ka’oje ne ya bayyana hakan a taron manema labarai da suka gudanar a Sakkwato a ranar Litinin inda ya ce, ko kadan dattawan Katsina ba su da kowace irin damar kalubalantar ko wane irin matakin da gwamnatin da ke kan mulki ta dauka saboda a baya sun kasa kalubalantar matakan da ba daidai ba a mulkin Shugaba Muhammadu Buhari.

  • Cire Tallafin Fetur: Ma’aikatan Jihar Jigawa Sun Ki Amincewa Da Karin Albashin Naira 10,000
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Mata Na Gudanar Da Zanga-zanga Kan Tsananin Yunwa Da Tsadar Rayuwa A Neja

Ka’oje ya bayyana cewar duk da yawaitar asarar rayuka da dukiyoyi da tabarbarewar tattalin arzikin Arewa, babu wani dattijon Arewa daga Katsina da ya fito ya yi magana kan gurbatattun manufofin da tsohuwar gwamnati ta dauka wadanda suka illata Arewa da ‘yan Arewa.

Kungiyar datawan Katsina dai ta fito fili ta nuna rashin dacewar daukar wasu matakan gwamnati musamman dauke wasu muhimman sassan Babban Bankin Kasa da hukumar kula da filayen jiragen sama daga Abuja zuwa Lagas da kuma aikin fadada filin jirgin sama na Umaru Musa ‘Yar’Adua da ke Katsina.

“Duk da tsananin talauci, matsalolin tsaro da gallazawar siyasa da aka fuskanta a zamanin mulkin Buhari, dattawan Katsina ba su kalubalanci tsohuwar gwamnatin ba?

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

“Wata tambayar ita ce, yaushe ne dattawan Katsina suka zama masu sukar manufofin gwamnatin Tarayya? Mutane da dama sun rasa rayuka da dukiyoyi, sha’anin noma ya tsaya cik kamar yadda dukkanin al’amurran rayuwar al’umma suka tabarbare saboda rashin tsaro da rashin iya jagorancin Buhari amma dattawan Katsina ba su taba nuna damuwar gyara lamurran ba?”

Kungiyar ta ce ta na goyon bayan kalaman Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle da ya ce wa dattawan Katsina da sauran kungiyoyi irin nasu da su ba da himma ga hadin kan kasa, su dakatar da kokarin zazafa siyasa ta hanyar kalaman da ba su dace kan Shugaba Tinubu ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dattawan Arewasiyasar NijeriyaTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

AFCON 2023: Ciwon Ciki Ka Iya Hana Osimhen Buga Wasan Gobe

Next Post

Rikicin Cikin Gida: Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano Ta Kama Ɗan Bindiga Da Ya Tsere Wa ‘Yan’uwansa

Related

Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

57 minutes ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

2 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

3 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

4 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

8 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

16 hours ago
Next Post
Rikicin Cikin Gida: Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano Ta Kama Ɗan Bindiga Da Ya Tsere Wa ‘Yan’uwansa

Rikicin Cikin Gida: Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano Ta Kama Ɗan Bindiga Da Ya Tsere Wa 'Yan'uwansa

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.