• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar ‘Yan Ta’adda Ta Ansaru Ta Ce Ba Ita Ta Kai Hari Kan Jirgin Kasan Abuja-Kaduna Ba

byMuhammad
3 years ago
Kungiyar

Ƙungiyar ‘Yan ta’adda ta Ansaru mai alaƙa da Kungiyar Al-Qaeda da ke ayyukanta a arewa maso yammacin Najeriya ta yi watsi da zargin da ake mata na hannu a harin da aka kai kan jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna ranar 28 ga watan Maris din 2022.

Kafar yada labari ta BBC ta rawaito cewa, a ƙalla mutum tara ne suka mutu a harin, sannan an sace wasu, wasu kuma suka ɓata.

  • Jami’an DSS Sun Cafke Wani Babban Kwamandan ISWAP A Kano
  • Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Ansaru ta ƙaryata zargin ne a wani saƙo na bidiyo da ta saki ranar 12 ga watan Yuni a shafukanta na Telegram da RocketChat.

Mai magana a cikin bidiyon ya yi jawabin ne da Larabci sannan ya yi da Hausa.

An ga a ƙalla mutum bakwai a bidiyon dukkansu sanye da takunkumin rufe fuska kuma suna ɗauke da bindigogi.

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Mutumin da ke bayanin wanda ba a iya gane shi, ya tsaya a tsakiya ne yana magana kan abin da ya kira “labarin ƙarya da yake yaɗuwa cewa ƙungiyar Ansarul al-Muslimin fi bilad al-Sudan (cikakken sunan ƙungiyar) ta ɗauki alhakin kai harin jirgin ƙasan.”

Ya ƙara da cewa “wannan ƙarya ce tsagwaronta wacce ba ta da tushe.”

Ya ce Ansaru ba ta da hannu ko kaɗan a harin jirgin ko sace fasinjojinsa.

Hukumomi a Nijeriya sun zargi Ansaru, wacce ke ayyukanta a yankin, da kuma ƙungiyar Boko Haram, wacce take da ƙarfi a arewa maso gabas, da hannu a kai wa jirgin ƙasan hari, ko dai kai tsaye ko kuma ta hanyar hada kai da ƴan bindigar da suke ayyukansu a yankin.

Ƴan bindigar sun yi ta sakin bidiyo da hotuna na mutanen da aka kama a jirgin tun bayan harin.

Mai magana a madadin Ansaru din ya ce an tsara “labarin ƙaryar” ne don a zubar wa ƙungiyar mutunci, inda ya jaddada cewa tana ƙoƙarin kaucewa cin zarafin ƴan yankin kuma tana taɓa waɗanda suke adawa ko fito na fito da ita ne kawai.

Tun bayan da ta fara ayyukanta a yankin arewa maso yammacin Nijeriya a farko-farkon shekarar 2021, a lokacin da ta bayyana mubaya’arta ga ƙungiyar al-Qaeda, Ansaru ta matsa wajen nesanta kanta da amfani da tsauraran hanyoyin masu ikirarin jihadi kamar su Boko Haram da IS da kuma ayyukan ƴan binciga.

A wani saƙonta na baya-baya, Ansaru ta nanata cewa tana neman hadin kan mutane ne ta hanyar da’awa maimakon yaƙarsu.

Mai maganar ya ce Ansaru ta yi amannar cewa harin jirgin ƙasan ba shi da alaƙa da jihadi kuma yin hakan ma jawo fitina ne kuma ya saɓa wa Musulunci da aƙidar masu jihadi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Mai Yiwuwa Ne Matakan Sin Na Iya Maida Komadar Tattalin Arzikin Duniya

Mai Yiwuwa Ne Matakan Sin Na Iya Maida Komadar Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version