• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kura Ta Turnike Majalisar Dattawa Kan Nadin Shugaban Marasa Rinjaye

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kura ta turnike zauren majalisar dattawa kan gwagwarmayar neman mukamin shugaban marasa rinjaye.

Kurar ta turnike ne bayan da rikicin kujerar shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa ya haifar da rashin jituwa a tsakanin sanatocin ‘yan jam’iyyar adawa na kokarin kaka ba musu shugabancin.

  • Hajji 2023: Tinubu Ya Bukaci Alhazai Da Su Kara Hakuri Da Halin Matsi Da Takura Da Suke Ciki

A majalisar dattawa ta 10, APC tana da sanatoci 59, PDP tana da 36, LP tana da 8, SDP na da 2, NNPP tana da 2, YPP na da 1, APGA na da 1.

Manyan mukamai hudu da aka ware wa jam’iyyun adawa a Majalisar Dattawa su ne, shugaban marasa rinjaye, mataimakin shugaban marasa rinjaye, mai tsawatarwa na marasa rinjaye da mataimakin mai tsawatarwa.

A wani yunkuri na samun hadil kai abokansa a matsayin shugaban marasa rinjaye a zauren majalisar dattawa, tsohon gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike ya gana da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio a ranar Alhamis da ta gabata.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Ganawar ya gudana ne a zauren majalisar na tsawan awanni da dama. Wike ya bar majalisar ne da misalin karfe 6:30 na yamma ba tare da ya yi magana da manema labarai ba.

An ce tsohon gwamnan Jihar Ribas ya bukaci abokinsa, Kingsley Chinda a matsayin shugaban marasa rinjaye a majalisar wakilai, duk da cewa har yanzu ba a tabbatar da shi ba.

Sai dai PDP da ke da kujeru mafi rinjaye a ‘yan majalisar dattawa 36 daga cikin jam’iyyun adawa, ta sha alwashin yin tir da duk wani makirci da jam’iyyar APC mai mulki ko wasu masu ruwa da tsaki za su yi na kulla alaka da ‘yan tsiraru a majalisar dattawa domin nada shugaban marasa rinjaye.

Har ila yau, ‘yan majalisar daga bangaren ‘yan adawar sun ce suna sane da matakin kutse a ciki da wajen majalisar dattawa ake yi na raba kan ‘yan tsirarun jam’iyyu da kuma samar musu da shugabancin da bai dace ba. Duk da haka, sun ba da tabbacin cewa makircin ba zai yi tasiri ba.

Da yake zantawa da Jaridar Daily Trust a jiya, Sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba, ya ce ‘yan Nijeriya sun tabbatar da cewa jam’iyyar PDP tare da sanatocinta za su kafa wasu tsirarun shugabannin da za su tabbatar da raba madafun iko da kuma tantancewa.

Ya ce, “Jam’iyyarmu jam’iyya ce take da tsari kuma muna bin ka’idojinmu. A kan batun shugabancin marasa rinjaye a Majalisar Dattawa, PDP na tuntubar sanatocinta bisa tsarin dimokuradiyyarmu.

“Abin da ya fi dacewa a gare mu a jam’iyya shi ne, samun shugabancin masara rinjaye da zai tabbatar da tsayayyen adawa a majalisar dattawa da kuma maslahar ‘yan Nijeriya baki daya.

“Za mu mai da hankali kan tabbatar da cewa an bi tsarin dimokuradiyya da kuma ka’idojin raba madafun iko. Muna tuntubar jama’armu kuma bayaninsu ya yi daidai da matsayinmu na jam’iyya, muna tattaunawa da su, kuma a karshe za mu fitar da matsayinmu na samun tsayuwar adawa mai karfi a cikin majalisar kasa.

“Za mu tabbatar an bi ka’idojin tsarin mulki,” in ji shi.

Tun a ranar Asabar da ta gabata, ‘yan majalisar dattawa daga jam’iyyun adawa sun sha alwashin yin fatali da duk wani yunkuri na dora musu shugaban marasa rinjaye wanda bai dace ba a zauren majalisar dattawa.

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa na ‘yan majalisar da suka fitar sun ce ‘yan adawa za su zabi shugabanninsu ne bayan tattaunawa da jam’iyyun siyasarsu ba tare da tsangwama daga masu yin kutse ga tsarin dimokuradiyya ba.

Sun jadadda cewa har yanzu babu wani sanata da aka amince da shi ko aka zaba a matsayin shugaban marasa rinjaye.

Sanarwar ta samu sa hannun hadin gwiwar Mohammed Adamu Aliero, Henry Seriake Dickson, Aminu Waziri Tambuwal, Abdul Ningi, Patrick Abba Moro, Ezenwa Francis Onyewuchi, Sumaila Kawu da kuma Ifeanyi Patrick Ubah.

Ta ci gaba da cewa, “Ga zuwa yanzu dai, ‘yan jam’iyyun adawa a zauren Majalisar Dattawan ana kokarin raba kan ‘yan adawa kuma yi musu zagon-kasa wajen kakaba musu shugabanni.

“Mun yi alkawarin yin aiki tare da sabbin shugabannin majalisar dattawa da bangaren zartarwa don isar da kyakkyawan shugabanci ga al’ummar Nijeriya. Don haka muna ba da shawara da lura cewa ka da su taimaka wa wata kungiya a ciki ko wajen majalisar dattawa don raba kan ‘yan adawa.

“Sanatocin jam’iyyun adawa za su gana idan majalisar dattawa ta dawo daga hutu, kuma za mu tuntubi jam’iyyun siyasarmu wajen zaben shugabanninmu ba tare da tsangwama daga masu kutse a dimokuradiyya a ciki ko wajen majalisar dattawa ba.

“Don kauce wa shakku, har yanzu babu wani sanata da aka amince da shi ko aka zaba a matsayin shugaban marasa rinjaye saboda bin tsarin da ya dace kamar yadda dukkanin ‘yan dawa suka amince a taronsu na karshe.

“Ba za lamunci duk wani yunkurin kafa mulkin kama-karya na jam’iyya mai mulki ba.
“Muna kira ga dukkan ‘yan jam’iyyun siyasa marasa rinjaye da su yi aiki tare cikin hadin kai don kare tsarin dimokuradiyya na majalisar dattawa da na Nijeriya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mene Ne Ma’anar Sakon Xi Jinping Kan Zagayowar Ranar Kafuwar JKS?

Next Post

JKS Tana Da Mambobi Sama Da Miliyan 98 Ya Zuwa Karshen 2022

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

3 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

1 week ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
JKS Tana Da Mambobi Sama Da Miliyan 98 Ya Zuwa Karshen 2022

JKS Tana Da Mambobi Sama Da Miliyan 98 Ya Zuwa Karshen 2022

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.