ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Kura

A ‘yan shekarun nan, wasu ‘yan siyasa da kafofin watsa labaru na kasashen yamma suna ta yada zancen cewa wai “kasar Sin ta dana wa kasashen Afirka tarkon bashi”. Sai dai wani rahoton bincike na baya-bayan nan da wata kungiya mai zaman kanta ta kasar Burtaniya, mai suna “Debt Justice”, ta fitar, ya nuna akasin haka. 

 

Binciken, wanda ya shafi kasashe daban daban guda 88, ya nuna cewa, a tsakanin shekarar 2020 zuwa ta 2025, kaso 39% na kudin basussukan waje da kasashe masu karamin karfi suka biya, ya shiga aljihun hukumomi masu ba da lamuni na kasuwanci, kana kaso 34% na kudin ya koma wajen cibiyoyi masu wakiltar moriyar bangarori daban daban, yayin da kaso 13% kacal aka biya cibiyoyi masu ba da lamuni na jama’a da masu zaman kansu na kasar Sin. Dangane da batun, Tim Jones, darektan tsare-tsare a “Debt Justice”, ya ce: “Shugabannin kasashen yammacin duniya suna dora wa kasar Sin alhakin matsalar basussukan da ake bin kasashen Afirka, amma wannan wani mataki ne na karkatar da hankali kawai. Hakika, bankuna, da kamfanoni masu sarrafa kadarori, da masu kula da cinikin man fetur, na kasashen yamma, su ne wadanda ya kamata su dauki mafi yawan alhakin.”

ADVERTISEMENT
  • Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface
  • Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

Rahoton ya nuna cewa galibin masu ba da lamuni a kasashe masu karamin karfi sun fito ne daga kasashen yammacin duniya, kuma kusan dukkansu na son daukar manufa mai tsauri, da kokarin neman mafi yawan riba. Misali, katafaren kamfanin cinikin ma’adinai na Glencore ya dade da kin amincewa da yafewa kasar Chadi duk wani bashi da yake binta. Ban da haka, ko da yake an shafe shekaru hudu da rabi ana tattaunawa, har yanzu Zambia ta kasa cimma wata yarjejeniyar yafe basussuka da wasu masu ba da lamuni masu zaman kansu suke binta, ciki har da bankin Standard Chartered na kasar Burtaniya. A bayyane wannan tsarin basussuka dake nuna taurin kai da kwadayi, da yadda masu ba da lamuni na kasashen yamma ke tsayawa kan karbar kudin ruwa mai yawa, da kuma samun riba cikin gajeren lokaci, su ne ainihin dalilan da ya sa kasashe masu tasowa fadawa cikin mawuyacin hali a fannin biyan bashi.

Sai dai me ya sa har kullum kasashen yamma suke son dora wa kasar Sin laifin “dana tarkon bashi”?

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Daƙile Kutsen ‘Yan Bindiga Na Iyakokin Jihar Kano

Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Na Daƙile Kutsen Ƙungiyar Ta’addanci Ta JNIM A Nijeriya

Dalili shi ne, kasar Sin ba ta son zama ‘yar amshin shata ta kasashen yamma. A kullum kasashe masu sukuni na yammacin duniya suna kallon kansu a matsayin masu tsara ka’idoji a duniya, inda suke bukatar kasar Sin da sauran kasashen da tattalin arzikinsu ke tasowa, su bi tsare-tsarensu na ba da bashi. Sai dai kasar Sin tana da ra’ayinta na kanta.

Bayan shiga karni na 21, sai hukumomin kasashen yamma suka fara rage bashin da suke baiwa kasashen Afirka kai tsaye. A nata bangare, kasar Sin ta lura da yanayin da kasashen Afirka suke ciki na fama da koma bayan tattalin arziki, don haka ta gabatar da tsarin samar da rance don taimaka wa kasashen Afirka raya kansu, bisa fasahohin da ta samu a fannin raya kai. Inda a wani bangare kasar Sin ta samar da dimbin bashin da wa’adin biyansu ke da tsawo, wadanda ruwansu ba shi da yawa, ga kasashen Afirka kai tsaye, yayin da a bangare na daban, kasar Sin da kasashen Afirka suke hadin gwiwa a kokarin gina kayayyakin more rayuwa, bisa amfani da rancen da kasar Sin ta samar. Wadannan al’amura sun nuna ra’ayin kasar Sin na kokarin amfanawa kowa yayin da ake hadin gwiwa.

Ban da haka, kasar Sin ta shiga shirin kungiyar G20 na saukaka matakan biyan bashi ga kasashe masu matsala. A sa’i daya, ba ta dauki dabarar kasashen yamma ta rage bashi bisa sanya wa kasashen Afirka wasu sharuda ba. Maimakon haka, Sin ta fi yin amfani da dabarar dakatar da biyan bashi da kudin ruwa dake tattare da bashin, da tabbatar da manufar tsawaita wa’adin biyan bashin ta hanyar shawarwari, wajen taimakawa kasashen da suke da bukata, dabarar da ta yi amfani gami da samar da sakamako mai kyau, yayin da ake kokarin gwada ta.

Kasar Sin tana amfani da dabaru da fasahohin da ta samu a fannin hada-hadar kudi yayin da take raya tattalin arzikinta, wajen taimakawa kasashen Afirka fid da kansu daga wani kangin yawan cin bashi ba tare da samun ci gaban ba, da dogaro kan matakan yafe bashi, domin kyautata dabarun amfani da kudin da aka samu, da inganta tsare-tsaren aiki. Sai dai a ganin kasashen yamma, matakin tamkar wata barazana ce ga babakeren da suka kafa a fannin hada-hadar kudi.

Saboda haka, ‘yan siyasa da kafofin watsa labaru na kasashen yamma suka fara alakanta kasar Sin da matsalar biyan bashi da wasu kasashe masu tasowa ke fuskanta. Sai dai, a hakika, matakin da suka dauka tamkar dai abin da Hausawa ke cewa ne wato “Kura za ta ce da kare maye”. (Bello Wang)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mutane 7 Ne Suka Rasu Sakamakon Zazzabin Cizon Sauro Da Taifod Ba Wata Sabuwar Cuta Ba – Gwamnatin Kano
Ra'ayinmu

Buƙatar Daƙile Kutsen ‘Yan Bindiga Na Iyakokin Jihar Kano

November 28, 2025
Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Na Daƙile Kutsen Ƙungiyar Ta’addanci Ta JNIM A Nijeriya
Ra'ayinmu

Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Na Daƙile Kutsen Ƙungiyar Ta’addanci Ta JNIM A Nijeriya

November 21, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
Ra'ayi Riga

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

November 4, 2025
Next Post
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.