ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Na Daƙile Kutsen Ƙungiyar Ta’addanci Ta JNIM A Nijeriya

by Leadership Hausa and Sulaiman
7 months ago
JNIM

A ranar 31 na watan Oktobar 2025, Kungiyar ‘Yan Ta’adda ta Jama’at Nusrat al-Islam wal-Muslimeen JNIM, ta yi ikirarin cewa, ta kaddamar da kanta cikin kasar nan.

Wannan ikirarin na ta, ya nuna tsagwaron sakacin da aka yi a fannin tsaron kasar, musamman duba da yadda kungiyar, masu tsatsauran ra’ayi, har suka iya  kutse a cikin kasar.

  • Akwai Bukatar Karfafa Hadaka Domin Ciyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa Gaba A Afirka —Dantsoho
  • Sin: Kome Zai Samu Yankin Taiwan Babu Ruwan Kasar Japan

Kungiyar wadda ke da akida irin ta Kungiyar Ta’addanci ta Al-Kaeda, ta shelanta cewa, ta hallaka Sojin kasar daya, yayin da ‘ya’yanta, suka yi wa tawagar dakarun soji, kwanton Bauna a Iyakar kasar Benin.

ADVERTISEMENT

 

Kazalika, wannan kutsen na kungiyar, ya nuna karara na irin sakacin tsaron kasar nan da har ayyukan kungiyar, ya tsallake yankin Sahel zuwa Afrika ta Yamma.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

 

Za a iya cewa, ta yi wannan kusten daidai da lokacin da Nijeriya, ke ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro da kuma yadda wasu kungiyoyi masu tsatsauran ra’ayi ke kai hare-hare kan wasu ‘yan kasar.

 

A nan, wannan Jaridar na yin mamaki kan yadda kungiyar ta As JNIM mai alaka da Al-Kaeda ke kara ba za ayyukanta a cikin kasar.

A saboda hakan Jaridar na ganin ya zama wajbi mahukuntan tsaron kasar, da su tabbatar da sun karfafa tsaro, a iyakokin kasar

Kungiyar ta JNIM, an kirkiro da ita ne, a watan Maris na 2017, wadda kuma ta yi hadaka da kungiyar Al-Kaeda.

Bugu da kari, Majalisar Tsaro ta Majalisar Dinkin Duniya, ta ayyana kungiyar ta JNIM, a matsayin wani reshe na Al-Kaida, da ke a kasar Mali.

Zallaka, Gidauniyar kafar yada labarai ta JNIM, ta yi wallafa ikirarin cewa, dakarun kungiyar sun samu nasarar yiwa sojojin kwanton Bauna ta hanyar dasa Bam a Iyakar Benin, wanda hakan, ya janyo mutwar soja daya.

Wannan ayyukan ta’addancin kungiyar, ya yi daidai da, irin salon da ta yi watan Yulin 2025, wanda ta kai hare-haren da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 54 a kasar Burkina Faso, wasu 36 a kasar Mali, da kuma wasu bakwai, a Jamhuriyyar Nijar, ta hanyar yin amfani da Iyakar Markoye.

Kazalika, kungiyar na yin amfani da Jirage marasa matuka, wajen kai hare-harensu, wadda kuma Al-Kaeda ce, ke tallafa wa mata da makamai da kuma kudade, domin aikata ta’asarsu.

Iyakar Benin da Nijeriya, ta kasance, wata mashiga ta yin fasakwarin makamai da muggana kayan maye, wanda hakan ya zama babbar hanyar da kungiyar ke yin amfani da ita.

Wani rahoton ta UNODC ta fitar a 2025 ya nuna cewa, an kiyasta cewa, an shigo da kaso 70 na kananan makamai ta Iyakar Benin da Nijeriya,

Hakazalika, wani rahoton Bankin Duniya ya sanar da cewa, talauci, ya Arewacin Nijeriya, ya sanya irin wadannan kungiyoyin ta’addacin daukar hayar wasu shiga cikin irin wadannan kungiyoyin ta’addancin.

Wannan Jaridar na da yakin cewa, domin a dakile ayyuan kutsen irin wadannan kungiyoyin ta’addancin, ya zama wajbi mahukunta a kasar nan, su amfani da kimiyyar fasahar zamani wajen tabbatarwa da karfafa tsaro, a iyakon kasar.

Bugu da kari, ya zama wajbi, a sanya na’urorin zamani na sanya ido da kuma yin amfani da Jiragen sama, marasa matuka domin tabbatar da tsaro.

Kazalika, ya kamata mahukuntan kasar, su yi koyi da salon da jihar Sokoto ta kirkiro da shi, na karrarfafa tsaro a iyakokin jihar.

Ya kuma kamata a yi amfani da salon kungiyar ECOWAS, na gudanar da aikin sintiri na hadaka domin dakile shigorar ‘yan ta’adda daga yankin Sahel inda kwararowarsu, ta kai kaso da shigo da makamai, ta kai 60.

Bugu da kari, akwai bukatar a zuba kudade masu dimbin yawa a shekarar 2026, cikin Cibiyar Dakile Shigo da Kananan Makai ta kasa, tare da kuma tabbatar da ana yin aiki kafada da kafada a tsakanin Hukumomin Tsaro, musaman domin a dakile kutsen kungiyoyin ‘yan ta’adda zuwa cikin kasar nan.

Haka, ya kamata mahukunta a kasar, su kirkiro da shirye-shiye a cikin alumma, kamar dai a jihar Borno, domin a bai wa matasa horon koyon sana’aion hannu domin kare su, daga jan ra’ayin kungiyar ‘yan ta’adda na shiga cikin kungiyoyin.

Da irin wannan salon jan ra’ayin wasu matasan ne, har ta kai ga kungiyar Al-Kaeda ta yi fice, wajen janyo matasa a cikinta.

Wasu daga cikin kwararru, musamman da ke yin fashin baki kan aukuwar rikice-rikice, suna ganin yin yafiya ga ‘yan ta’adda da suka tuba suka kuma ajiya makamansu, hakan zai taimaka, wajen rage aikata ta’addanci.

Duba da yadda kungiyar ta JNIM da ke da alaka da Al-Kaeda, ta yi kutse a cikin kasar nan, ya zama wajbi, mahukunta a kasar, su dauki matakan gaggawa domin a taka mata birki, wanda hakan zai bai wa kasar samun cikakken ikon bai wa iyakon kariya.

JNIM
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
JNIM
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • Sulaiman
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Yunkurin Japan Na Komawa Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ba Zai Yi Nasara Ba

Yunkurin Japan Na Komawa Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ba Zai Yi Nasara Ba

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.