ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Ɗaukar Matakin Gaggawa Na Daƙile Kutsen Ƙungiyar Ta’addanci Ta JNIM A Nijeriya

by Leadership Hausa and Sulaiman
10 months ago
JNIM

A ranar 31 na watan Oktobar 2025, Kungiyar ‘Yan Ta’adda ta Jama’at Nusrat al-Islam wal-Muslimeen JNIM, ta yi ikirarin cewa, ta kaddamar da kanta cikin kasar nan.

Wannan ikirarin na ta, ya nuna tsagwaron sakacin da aka yi a fannin tsaron kasar, musamman duba da yadda kungiyar, masu tsatsauran ra’ayi, har suka iya  kutse a cikin kasar.

  • Akwai Bukatar Karfafa Hadaka Domin Ciyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa Gaba A Afirka —Dantsoho
  • Sin: Kome Zai Samu Yankin Taiwan Babu Ruwan Kasar Japan

Kungiyar wadda ke da akida irin ta Kungiyar Ta’addanci ta Al-Kaeda, ta shelanta cewa, ta hallaka Sojin kasar daya, yayin da ‘ya’yanta, suka yi wa tawagar dakarun soji, kwanton Bauna a Iyakar kasar Benin.

ADVERTISEMENT

 

Kazalika, wannan kutsen na kungiyar, ya nuna karara na irin sakacin tsaron kasar nan da har ayyukan kungiyar, ya tsallake yankin Sahel zuwa Afrika ta Yamma.

LABARAI MASU NASABA

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG

 

Za a iya cewa, ta yi wannan kusten daidai da lokacin da Nijeriya, ke ci gaba da fuskantar kalubalen rashin tsaro da kuma yadda wasu kungiyoyi masu tsatsauran ra’ayi ke kai hare-hare kan wasu ‘yan kasar.

 

A nan, wannan Jaridar na yin mamaki kan yadda kungiyar ta As JNIM mai alaka da Al-Kaeda ke kara ba za ayyukanta a cikin kasar.

A saboda hakan Jaridar na ganin ya zama wajbi mahukuntan tsaron kasar, da su tabbatar da sun karfafa tsaro, a iyakokin kasar

Kungiyar ta JNIM, an kirkiro da ita ne, a watan Maris na 2017, wadda kuma ta yi hadaka da kungiyar Al-Kaeda.

Bugu da kari, Majalisar Tsaro ta Majalisar Dinkin Duniya, ta ayyana kungiyar ta JNIM, a matsayin wani reshe na Al-Kaida, da ke a kasar Mali.

Zallaka, Gidauniyar kafar yada labarai ta JNIM, ta yi wallafa ikirarin cewa, dakarun kungiyar sun samu nasarar yiwa sojojin kwanton Bauna ta hanyar dasa Bam a Iyakar Benin, wanda hakan, ya janyo mutwar soja daya.

Wannan ayyukan ta’addancin kungiyar, ya yi daidai da, irin salon da ta yi watan Yulin 2025, wanda ta kai hare-haren da ya yi sanadiyar mutuwar mutane 54 a kasar Burkina Faso, wasu 36 a kasar Mali, da kuma wasu bakwai, a Jamhuriyyar Nijar, ta hanyar yin amfani da Iyakar Markoye.

Kazalika, kungiyar na yin amfani da Jirage marasa matuka, wajen kai hare-harensu, wadda kuma Al-Kaeda ce, ke tallafa wa mata da makamai da kuma kudade, domin aikata ta’asarsu.

Iyakar Benin da Nijeriya, ta kasance, wata mashiga ta yin fasakwarin makamai da muggana kayan maye, wanda hakan ya zama babbar hanyar da kungiyar ke yin amfani da ita.

Wani rahoton ta UNODC ta fitar a 2025 ya nuna cewa, an kiyasta cewa, an shigo da kaso 70 na kananan makamai ta Iyakar Benin da Nijeriya,

Hakazalika, wani rahoton Bankin Duniya ya sanar da cewa, talauci, ya Arewacin Nijeriya, ya sanya irin wadannan kungiyoyin ta’addacin daukar hayar wasu shiga cikin irin wadannan kungiyoyin ta’addancin.

Wannan Jaridar na da yakin cewa, domin a dakile ayyuan kutsen irin wadannan kungiyoyin ta’addancin, ya zama wajbi mahukunta a kasar nan, su amfani da kimiyyar fasahar zamani wajen tabbatarwa da karfafa tsaro, a iyakon kasar.

Bugu da kari, ya zama wajbi, a sanya na’urorin zamani na sanya ido da kuma yin amfani da Jiragen sama, marasa matuka domin tabbatar da tsaro.

Kazalika, ya kamata mahukuntan kasar, su yi koyi da salon da jihar Sokoto ta kirkiro da shi, na karrarfafa tsaro a iyakokin jihar.

Ya kuma kamata a yi amfani da salon kungiyar ECOWAS, na gudanar da aikin sintiri na hadaka domin dakile shigorar ‘yan ta’adda daga yankin Sahel inda kwararowarsu, ta kai kaso da shigo da makamai, ta kai 60.

Bugu da kari, akwai bukatar a zuba kudade masu dimbin yawa a shekarar 2026, cikin Cibiyar Dakile Shigo da Kananan Makai ta kasa, tare da kuma tabbatar da ana yin aiki kafada da kafada a tsakanin Hukumomin Tsaro, musaman domin a dakile kutsen kungiyoyin ‘yan ta’adda zuwa cikin kasar nan.

Haka, ya kamata mahukunta a kasar, su kirkiro da shirye-shiye a cikin alumma, kamar dai a jihar Borno, domin a bai wa matasa horon koyon sana’aion hannu domin kare su, daga jan ra’ayin kungiyar ‘yan ta’adda na shiga cikin kungiyoyin.

Da irin wannan salon jan ra’ayin wasu matasan ne, har ta kai ga kungiyar Al-Kaeda ta yi fice, wajen janyo matasa a cikinta.

Wasu daga cikin kwararru, musamman da ke yin fashin baki kan aukuwar rikice-rikice, suna ganin yin yafiya ga ‘yan ta’adda da suka tuba suka kuma ajiya makamansu, hakan zai taimaka, wajen rage aikata ta’addanci.

Duba da yadda kungiyar ta JNIM da ke da alaka da Al-Kaeda, ta yi kutse a cikin kasar nan, ya zama wajbi, mahukunta a kasar, su dauki matakan gaggawa domin a taka mata birki, wanda hakan zai bai wa kasar samun cikakken ikon bai wa iyakon kariya.

JNIM
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya
JNIM
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

JNIM
Ra'ayinmu

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

August 14, 2026
Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG
Ra'ayinmu

Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG

July 31, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Next Post
Yunkurin Japan Na Komawa Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ba Zai Yi Nasara Ba

Yunkurin Japan Na Komawa Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ba Zai Yi Nasara Ba

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.