ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Daƙile Kutsen ‘Yan Bindiga Na Iyakokin Jihar Kano

by Leadership Hausa and Sulaiman
6 months ago
Kano

Ci gaba da samun karuwar hare-hare kan al’umomin da ke a garurunwan iyaka da jihar da wasu jihohi, lamarin na kara jefa fargaba a cikin jama’a.

A saboda haka, akwai matukar bukatar a hada karfi da karfe, domin a kawo karshen kalubalen rashin tsaro, da tuni, ya zamowa kasar tamkar wani karfen Kafa, musamman a jihohin da ke a Arewa ta Yamma da kuma a jihohin da ke a Arewa ta Tsakiya

  • Tinubu Da Shugabannin ECOWAS Sun Gudanar Da Taron Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau
  • Sarkin Musulmi Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi

Kazalika, wasu alumomin da ke a jihohi kamarsu, Zamfara, Katsina, Kebbi da Sokoto, na ci gaba da kokakwa, kan yawan hare-haren da ‘yanbindiga ke kai masu, ind hare-haren, suka auka a wasu yankuna na Shanono da ke a Kano, wanda suke da iyaka da, musamman Katsina.

ADVERTISEMENT

Sai dai, wasu da ke a cikin alummomin na garin Shanono, sun tabbatar da cewa, tun a 2022 ne, ake kai masu hare-haren, inda a yayin hare-haren, aka kashe wasu, wasu kuma aka tarwatsasu daga matsugunansu, wasu kuma aka sace Sahnunsu.

Hakazalika, abin bakin ciki ne, kan samu karuwar hare-haren a Tsanyawa, Shanono, Bagwai, Gwarzo, da Karaye, da ke a iyaka da Katsina, inda lamarin, ya kuma ba zu, daga Katsina zuwa Kano.

LABARAI MASU NASABA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

Bugu da kari, an ci gaba da samun karuwar kai hare-hare da kuma yin garkuwa da mutane a yankin  Faruruwa da ke karamar hukumar Shanono, wanda har da wasu mata da aka sace.

Aukuwar hare-haren, sun sanya alumomin da ke a yankunn Tudun Fulani, Malami, Unguwar Kudu, ’Yan Kwada, Santar Abuja, Kulki, Unguwar Tsamiya da Goron Dutse, da sauransu, tserewa, daga matsugunansu.

Wani abin takaicin shi ne, duk da yin yarjejeniya samar da zaman lafiya da wasu alumomin da ke a jihar Katsina, inda akalla kananan hukumomi 18, suka kulla wannan yarjejiniar da ‘yan bindigar, amma sai hare-haren, suka kara zafafa.

Ayar tambaya a nan ita ce, idan har da gaske ne, wannan yarjejeniyar, da gaske ne, amma mai ya sanya, ‘yan bindigar suka karkatar da Akalarsu,  zuwa kai hare-hare a jihar Kano?

Hakan ya nuna a zahairi cewa, kulla yarjejeniyar da ‘yan bindigar tamkar alumomin, sun hakawa kawunansu, wani Kabari ne.

Karin wani abin dubi shi ne, yadda daukacin ‘yanbindigar, suka halarci wajen kulla yarjejeniyar,  sabe da muggan makamansu, a kafada.

Mun sha fada ba tare da wata tamtama ba cewa, mafita kan wannan matsalar ta rashin tsaron shi ne, hukumomin tsaron kasar, su kara kaimi wajen kai hare-hare kan ‘yan bindigar, domin kawo karshen ayyukansu na rashin imani.

Idan har mahukunta suka ci gaba da yin sakaci kan ci gaba da samun karuwar ayyukan ‘yanbindigar a Kano, ba fata ba, idan ba a yi a hankali ba, lamarin zai iya munana, fiye da na jihohin Zamfara, Kebbi da Katsina.

Maganar gaskiya, ci gaba da samun karuwar hare-haren ‘yanbindigar kan alumomin da ke a iyakar Kano, hakan ya nuna cewa, ya zma waji, a tashi ka’in da na’in, domin tunkarar kalubalen na rashin tsaron.

Shin me ya sa, yake zama wahala ga jami’an tsaro, tare da hadaka da gwamnatocin da ke a Arewa ta Yamma, suka gaza hada karfi da karfe domin kawo karshen ayyukan na ‘yanbidiga da kuma aikata, suran manyan laifuka a jihohin?

A nan, za mu iya cewa, ga dukkan lamu, rashin yin hobbasan gwamnatocin da ke a wadannan jihohin na tunkarar matsalar ne, ya kara bai wa ‘yanbindigar karfin ci gaba da aikata, ta’asarsu, a jihohin.

Lokaci ya yi da gwamnatocin da ke a wadannan jihohin za su tashi kan jiki kan karfi, domin magance kai hare-haren da ke akuwa kan alumomin da ke zaune a iyakon su, musamman ta hanyar hada hannu da sauran hukumomin tsaro, domin a cimma wannan nasarar.

Bugu da kari, ya zama wajbi, gwamnatocin wadannan jihohin, su mayar da hankali wajen kare rayuka da dukiyoyin alumomin su, daga hare-haren na ‘yan bindigar, wadanda har yanzu, suke ci gaba da cin Karensu, babu babbaka.

Kazalika, duba da yadda hare-haren na ‘yanbidagar ya durkusar da tattalin arzikin alumomin da ke a yankin, ya zama wajbi, gwamnatocin da ke a wadannan jihohin, su lalubo da mafita kan kalubalen na rashin tsaron.

Ra’ayin wannan Jaridar a nan shi ne, ya zama wajbi gwamnatocin da ke a wadannan jihohin, su tashi tsaye wajen, musamman duba da cewa, a yanzu, an shigo cikin kakar rani ne, wanda hakan zai sanya jami’an tsaro, da ke ci gaba da yakar ‘yanbindigar, samun damar kutsawa har zuwa sansanonin ‘yanbindigar domin ragargazarsu.

Lokaci ya yi da za a kawo karshen wannan zubar da mutuncin kasar da ‘yanbidigar ke ci gaba da yi, a idon duniya, musamman a yankunan da suka yi kaka gida.

Kano
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe
Kano
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?
Ra'ayinmu

Shin Nijeriya Ta Shirya Tunkarar Dawowar Annobar Ebola?

May 29, 2026
Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan
Labarai

Buƙatar Samar Da Alƙibla Ta Musamman Ga Gidajen Gyaran Hali Na Ƙasar Nan

May 22, 2026
Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
Ra'ayinmu

Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

May 15, 2026
Next Post
Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani

Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.