ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Daƙile Kutsen ‘Yan Bindiga Na Iyakokin Jihar Kano

by Leadership Hausa and Sulaiman
9 months ago
Kano

Ci gaba da samun karuwar hare-hare kan al’umomin da ke a garurunwan iyaka da jihar da wasu jihohi, lamarin na kara jefa fargaba a cikin jama’a.

A saboda haka, akwai matukar bukatar a hada karfi da karfe, domin a kawo karshen kalubalen rashin tsaro, da tuni, ya zamowa kasar tamkar wani karfen Kafa, musamman a jihohin da ke a Arewa ta Yamma da kuma a jihohin da ke a Arewa ta Tsakiya

  • Tinubu Da Shugabannin ECOWAS Sun Gudanar Da Taron Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau
  • Sarkin Musulmi Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi

Kazalika, wasu alumomin da ke a jihohi kamarsu, Zamfara, Katsina, Kebbi da Sokoto, na ci gaba da kokakwa, kan yawan hare-haren da ‘yanbindiga ke kai masu, ind hare-haren, suka auka a wasu yankuna na Shanono da ke a Kano, wanda suke da iyaka da, musamman Katsina.

ADVERTISEMENT

Sai dai, wasu da ke a cikin alummomin na garin Shanono, sun tabbatar da cewa, tun a 2022 ne, ake kai masu hare-haren, inda a yayin hare-haren, aka kashe wasu, wasu kuma aka tarwatsasu daga matsugunansu, wasu kuma aka sace Sahnunsu.

Hakazalika, abin bakin ciki ne, kan samu karuwar hare-haren a Tsanyawa, Shanono, Bagwai, Gwarzo, da Karaye, da ke a iyaka da Katsina, inda lamarin, ya kuma ba zu, daga Katsina zuwa Kano.

LABARAI MASU NASABA

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG

Bugu da kari, an ci gaba da samun karuwar kai hare-hare da kuma yin garkuwa da mutane a yankin  Faruruwa da ke karamar hukumar Shanono, wanda har da wasu mata da aka sace.

Aukuwar hare-haren, sun sanya alumomin da ke a yankunn Tudun Fulani, Malami, Unguwar Kudu, ’Yan Kwada, Santar Abuja, Kulki, Unguwar Tsamiya da Goron Dutse, da sauransu, tserewa, daga matsugunansu.

Wani abin takaicin shi ne, duk da yin yarjejeniya samar da zaman lafiya da wasu alumomin da ke a jihar Katsina, inda akalla kananan hukumomi 18, suka kulla wannan yarjejiniar da ‘yan bindigar, amma sai hare-haren, suka kara zafafa.

Ayar tambaya a nan ita ce, idan har da gaske ne, wannan yarjejeniyar, da gaske ne, amma mai ya sanya, ‘yan bindigar suka karkatar da Akalarsu,  zuwa kai hare-hare a jihar Kano?

Hakan ya nuna a zahairi cewa, kulla yarjejeniyar da ‘yan bindigar tamkar alumomin, sun hakawa kawunansu, wani Kabari ne.

Karin wani abin dubi shi ne, yadda daukacin ‘yanbindigar, suka halarci wajen kulla yarjejeniyar,  sabe da muggan makamansu, a kafada.

Mun sha fada ba tare da wata tamtama ba cewa, mafita kan wannan matsalar ta rashin tsaron shi ne, hukumomin tsaron kasar, su kara kaimi wajen kai hare-hare kan ‘yan bindigar, domin kawo karshen ayyukansu na rashin imani.

Idan har mahukunta suka ci gaba da yin sakaci kan ci gaba da samun karuwar ayyukan ‘yanbindigar a Kano, ba fata ba, idan ba a yi a hankali ba, lamarin zai iya munana, fiye da na jihohin Zamfara, Kebbi da Katsina.

Maganar gaskiya, ci gaba da samun karuwar hare-haren ‘yanbindigar kan alumomin da ke a iyakar Kano, hakan ya nuna cewa, ya zma waji, a tashi ka’in da na’in, domin tunkarar kalubalen na rashin tsaron.

Shin me ya sa, yake zama wahala ga jami’an tsaro, tare da hadaka da gwamnatocin da ke a Arewa ta Yamma, suka gaza hada karfi da karfe domin kawo karshen ayyukan na ‘yanbidiga da kuma aikata, suran manyan laifuka a jihohin?

A nan, za mu iya cewa, ga dukkan lamu, rashin yin hobbasan gwamnatocin da ke a wadannan jihohin na tunkarar matsalar ne, ya kara bai wa ‘yanbindigar karfin ci gaba da aikata, ta’asarsu, a jihohin.

Lokaci ya yi da gwamnatocin da ke a wadannan jihohin za su tashi kan jiki kan karfi, domin magance kai hare-haren da ke akuwa kan alumomin da ke zaune a iyakon su, musamman ta hanyar hada hannu da sauran hukumomin tsaro, domin a cimma wannan nasarar.

Bugu da kari, ya zama wajbi, gwamnatocin wadannan jihohin, su mayar da hankali wajen kare rayuka da dukiyoyin alumomin su, daga hare-haren na ‘yan bindigar, wadanda har yanzu, suke ci gaba da cin Karensu, babu babbaka.

Kazalika, duba da yadda hare-haren na ‘yanbidagar ya durkusar da tattalin arzikin alumomin da ke a yankin, ya zama wajbi, gwamnatocin da ke a wadannan jihohin, su lalubo da mafita kan kalubalen na rashin tsaron.

Ra’ayin wannan Jaridar a nan shi ne, ya zama wajbi gwamnatocin da ke a wadannan jihohin, su tashi tsaye wajen, musamman duba da cewa, a yanzu, an shigo cikin kakar rani ne, wanda hakan zai sanya jami’an tsaro, da ke ci gaba da yakar ‘yanbindigar, samun damar kutsawa har zuwa sansanonin ‘yanbindigar domin ragargazarsu.

Lokaci ya yi da za a kawo karshen wannan zubar da mutuncin kasar da ‘yanbidigar ke ci gaba da yi, a idon duniya, musamman a yankunan da suka yi kaka gida.

Kano
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya
Kano
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Kano
Ra'ayinmu

Batun Shayar Da Jarirai Nonon Uwa Da Ƙalubalen Abinci Mai Gina Jiki

August 14, 2026
Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG
Ra'ayinmu

Buƙatar Kawo Ƙarshen Dogon Layi A Tashoshin Sayen Iskar CNG

July 31, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi
Ra'ayinmu

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Next Post
Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani

Allah Ya Bai Wa Annabi (SAW) Mu’ujizozi Fiye Da 2,000 A Alƙur’ani

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.