• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: Masu Bayyana Ra’ayi Sun Zargi USADA Da Yin Rufa-rufa

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Cgtn

Batun rufa-rufa game da dan wasan tseren Amurka Erriyon Knighton da aka zarga da amfani da abubuwa masu kara kuzari yayin wasa, ya bankado zargin da ake yiwa hukumar yaki da amfani da abubuwan kara kuzari yayin wasanni ta Amurka wato USADA da boye gaskiya, da yin fuska biyu, da amfani da karfin iko ba bisa ka’ida ba.

Game da hakan, wasu kuri’un al’umma da kafar CGTN ta tattara sun nuna kaso 95.57 bisa dari na al’ummun da suka bayyana ra’ayoyinsu daga sassa daban daban na duniya, na zargin USADA da yiwuwar rufe gaskiya kan ’yan wasan Amurka, da aka tabbatar sun yi amfani da abubuwa masu kara kuzari.

  • Hukumar Yaki Da Shan Maganin Kara Kuzari Yayin Wasanni Ta Duniya Ta Fallasa Ayyukan Amurka Game Da ’Yan Wasa Masu Keta Ka’idoji
  • Ya Kamata Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Karshen Matsin Rayuwa – Gwamnan Bauchi 

A watan Maris da ya shude, hukumar yaki da amfani da abubuwa masu kara kuzari yayin wasanni ta kasa da kasa WADA, ta samu Erriyon Knighton da laifin amfani da abubuwan kara kuzari, amma duk da haka hukumar USADA ta kyale shi ya shiga wasu wasanni ba tare da la’akari da hukuncin WADA ba. Sai dai kawai USADA ta ce wai dan wasan ya ci wani nama ne gurbataccen wanda ya sanya aka same shi da wancan laifi.

Amma a daya bangaren WADA ta fitar da sanarwa, inda ta ce ba ta taba baiwa hukumar USADA ikon barin irin wadannan ’yan wasa da aka kama da lafin su shiga gasanni ba, domin hakan zai iya zubar da kimar gasanni.

Game da hakan, sakamakon kuri’un jin ra’ayi na CGTN, sun nuna cewa kaso 90.15 na jama’ar da suka bayyana matsayar su na ganin Amurka ta rufe laifin Knighton, har ta ba shi damar shiga gasar Olympic ta birnin Paris, wanda hakan ya yi matukar gurgunta kima da makasudin gasanni. Har ila yau, kaso 96.54 bisa dari na masu bayyana ra’ayin na ganin abun da Amurka ta yi misali ne na yin fuska biyu. Yayin da wani kason da ya kai 95.63 bisa dari ke ganin da yawa daga yan wasan Amurka na gabatar da shaidun bogi na gwaje gwajen da aka yi musu.

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Bugu da kari akwai kaso mai yawa da ya kai 96.23 bisa dari dake ganin ya dace a kara yawan gwajin da ake yiwa ’yan wasan Amurka masu halartar gasar Olympic ta Paris, domin dawo da kima da kwarin gwiwar adalci tsakanin sassan kasa da kasa kan gasar.

An gudanar da kuri’un jin ra’ayin al’ummar na CGTN ne ta harsunan Turanci da Faransanci, da Larabci, da harsunan Sifaniya da Rasha, inda masu bayyana ra’ayi 14,580 suka fayyace matsayarsu cikin sa’o’i 16.
(Mai Fassara: Saminu Alhassan)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 
Daga Birnin Sin

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba
Daga Birnin Sin

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Yi Karar EU A WTO Kan Matakan Wucin Gadi Kan Motocin Lantarki Na Kasar Sin

Kasar Sin Ta Yi Karar EU A WTO Kan Matakan Wucin Gadi Kan Motocin Lantarki Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.