• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…

by Sulaiman and Sabo Ahmad
3 years ago
in Rahotonni
0
Kusan Shekara 100 Da Kafa Asibitin Kutare Na Kano, Amma…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram
  • Har Yanzu Galibin Mutane Ba Su Fahimci Muhimmancinsa Ba
  • AkwaiKarancin Ma’aikata
  • Wasu Makota Na Yi Masa Zagon Kasa
  • ‘Yan Sumoga Sun Addabi Harabarsa, In Ji Daraktansa

LEADERSHIP HAUSA ta yi tattaki zuwa Asibitin Kutare na Bela da ke kan hanyar Gezawa a karamar hukumar Tofa ta Jihar Kano, domin kawo wa masu karatunmu labari a kan halin da asibitin ke ciki, da kuma fahimtar da al’umma irin ayyukan kiwon lafiyar da yake yi domin ‘yan kasa su ci gajiyar asibitin.

Wakilinmu SABO AHMAD KAFIN-MAIYAKI ya zanta da Daraktan Shiyya na hukumar da ke kula da asibitocin Jihar Kano, shiyya ta daya, wadanda suka kunshi Asibitin Kutare na Bela, da Asibitin Zana da na Hakori, ABDULLAHI ISMA’ILA KWALWA. Ga dai yadda tattaunawar tasu ta kasance:

Darakta, barka da warhaka. Masu karatunmu za su so, ka gabatar da kanka.
Sunana Abdullahi Isma’ila Kwalwa. Ni ne Daraktan shiyya na hukumar da ke kula da asibitici a jihar Kano, shiyya ta daya da ke kula da Asibitin kutare na Bela da Asibitin Zana da Asibitin Hakori da kuma wasu asibiti guda uku kanana, wadanda suke kunshi asibitocin shiyyar guda shida.

Menene tarihin wannan asibitin kutare na Bela?
An kafa wannan asibiti a shekara ta 1930, lokacin Sarkin Kano, Abdullahi Bayero. An yi niyyar kafa wannan asibitin ne da a garin Sumaila, amma sai aka zo aka yi shi a wannan muhallin da kake ganinsa a halin yanzu, ganin cewa, a wannan gurin zai fi saukin shiga da fita, musamman ga wadanda ke nesa, amma saboda yanayin irin mutane da ke jiyya a wannan asibiti, ya zama an nesanta shi daga cikin al’ummar gari, yadda majiyayyata za su samu walwala ba tare da nuna tsangwama ba daga wasu al’umma. Asibitin Bela asibiti ne da ke da haraba mai fadin gaske. An debi wannan harabar ce, tun a wancan lokacin bisa hasashen duk loacin da aka bukaci fadada shi, za iya fadada shi ba tare da wata matsala ba.
A cikin shekara ta 1975, Gwamnan Jihar Kano Audu Bako a wancan lokacin ya zo ya yanki wani bangare na wannan asibiti, ya sa aka haka dam. Sai dai babban abin takaici shi ne, yadda wasu bata-gari ke neman hana ruwa gudu a wannan asibiti, musamman wasu daga cikin makotan asibitin, ta hanyar karkatar da wasu marasa lafiya zuwa wasu a sibitoci masu zaman kansu, wanda hakan na daga cikin abin da ya zame wan nan asibiti alakakai.
Tun daga wancan lokacin zuwa yanzu, asibitin ya kai kusan kimanin shekara dari da kafa shi, saboda haka, yana da dogon tarihi, tun lokacin Turawan milkin mallaka.
Tun daga wancan lokacin da aka kafa shi, ya ci gaba da samun ci gaba, inda bayan kasancewarsa asibitin kutare ya zama ana karbar haihuwa a cikinsa, an kuma samu dakin gwaje-gwaje da kuma dakin daukar hoto, samar da wadannan ayyuka da ake yi a wannan asibiti, sai aka daga darajarsa ya tashi daga asibitin kutare, ya zama Babban Asibiti. Saboda haka sai ya zama yana samar da lafiya ga yara da mata da sannan kuma ana kwanciya a cikinsa, sannan kuma asibitin na yin ayyukan riga-kafi.
Saboda haka ida aka dubi asibitin a halin yanzu za a iya cewa, ya samu ci gaban da majiyyata ke zuwa daga kowane sashi na kasar nan domin a kula da lafiyarsu, kuma daidai gwarwado suna samun biyan bukata.

Wadanne kakubale wannan asibiti ke fuskanta a halin yanzu?
Babban kalubalen da wannan asibiti ke fuskanta shi ne, karancin ma’aikata, a wannan asibitin muna da bangaren sha-ka-tafi, muna da kwararrun likitoci a bangaren fata, saboda haka, dukkan wani likita da zai tura majiyyaci kan aikin fata asibitin Bela zai tura, saboda muna da kwararrun lilitocin fata, a wannan asibitin, wanda ya sa al’umma daga ko’ina da suke da matsalar da ta shafi fata ke zuwa wannan asibitin.
Wannan ta sa nake ganin indai za a yi maganar babban kalubalen da wannan asibitin ke fuskanta bai wuce na rashin wadatattun ma’aikata ba.
Wani babban kalubale, ko kuma in ce babbar barazar da wannan asibitin ke fuskanta ita ce, har yau mutanen da ke makotaka da wannan asibiti ba su fahimci amfaninsa ba. Kusan shekara dari da kafa wannan asibitin amma har yanzu wasu da yawa daga cikin mutanen wajen ba su fahimci muhimmancin asibitin ba, musamman kan yadda za su bayar da gudummowa wajen ganin ya samu ci gaba, saboda haka ka da su dauka cewa, lallai sai gwamnati ce za ta taimaka wa wannan asibitin al’umma sun a suna da gudummowar da za su bayar.
Wata babbar matsala da wannan asibitin ke fuskanta daga wasu mazauna wannan yanki, shi ne yadda sukan bi sawun mara lafiya, yadda za su kwadaitar da shi ya bar wannan asibitin zuwa wani asibitin mai zaman kansa, yadda za su hada baki inda suka kai shi domin su sanu kudi, daga mara lafiya da kuma asibitin da suka kai majiyyaci.
Karin wani babban kalubalen da wannan asibitin ke fuskanta shi ne na tsaro, yadda wasu masu somoga da sauran wasu masu laifi kan keto ta harabar wannan asibiti, wanda hakan ke zaman wata babbar barazana ga wannan asibitin da kuma majiyyatan da ke cikinsa, musamman a wannan lokaci da ake fuskantar matsalar tsaro, kuma da ma wasu majiyyatan za ka samu baki ne, ba su san yanayin yankin ba, ka ga hakan na iya dagula musu lissafi ta hanyar jefa musu tsoro cikin zukatansu. Shi majiyyaci kullum ana bukatar ya samu kwanciyar hankali ba tashin hankali ba, domin fadawarsa cikin tashin ba zai taimaka masa ba wajen samun lafiyar da ya zo nema ba.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Wane sako kake da shi ga majiyyata da ke wannan Asibiti?
A gaskiya, majiyyata na kokari matuka, ka ga majiyyata kan zo daga nesa, kamar Nijar da Yobe da Maiduguri, kai kusan ko’ina a fadin kasar nan domin neman lafiya, kuma sukan zo ba tare da cewa, sun san wani a wannan gari ba, maganar neman lafiyar ce kawai ke kawo su.
Sai dai babban kiran da zan yi musu shi ne, su kara hakuri, yayin da suka zo wajen neman lafiya, kuma su daure su bi dokokin da likita ya kafa musu, domin su samu warakar da suka zo nema, sannan kuma su yi hankali da wasu mutane da ka iya zuwa wajensu, da niyyar cewa, za su taimake su, su kai su wani asibitin da za a kula da su, cikin gaggawa.

Akwai wani sako da kake da shi musamman ga masu hannu da shuni da ke kusa da kuma na nesa da wannan asibitin?
Babban sakona shi ne, musamman ga masu hannu da shuni, shi ne su yi amfani da damar da Allah ya ba su wajen taimaka wa wannan asibiti wanda dimbin al’umma ke amfana da shi. Domin kuwa da irin wannan gudummowarce wasu asibitoci suka bunkasa, bas a jiran gwamnati, musamman a wannan kasa idan muka lura, za a iya cewa, nauyi ya yi wa gwamnati yawa, saboda haka, akwai bukatar masu hannu da shuni su shiga sahun masu bayar da taimako ga wannan asibiti, mai dimbin tarihin da ya shafe kusan sheka dari yana gudanar da ayyukan lafiya.
Wane sako kake da shi ga al’ummar wannan yanki da wannan asibiti ke ciki, sakona shi ne su kara jin tsoron Allah, su tabbatar sun bayar da gudummowar gina wannan asibitin ba rusa shi ba, wannan kuma zai raimaka wajen su kansu mazauana yankin su kara samun ci gaba.
Ga gwamnati kuma, za mu iya cewa, kokarin da take wajen inganta wannan asibi na taimaka wa majiyyata wajen samun kulawar da ta kamata ga marasa lafiyar da suka zo nema daga mesa da kusa a dukkan fadin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Son Zuciyar Wasu Tsiraru Ya Haddasa Rashin Tsaro A NIjeriya – Alhaji Ibrahim

Next Post

Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

7 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

1 week ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

2 weeks ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 weeks ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

3 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

3 weeks ago
Next Post
Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu

Kamata Ya Yi Dalibai Su Maka Kungiyar ASUU A Kotu Kan Bata Musu Lokaci—Adamu Adamu

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.