• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamitin Tallafin Karatu Na Sanata Maidoki Ya Tantance Dalibai Sama Da 805 A Kebbi

by Umar Faruk
9 months ago
in Labarai
0
Kwamitin Tallafin Karatu Na  Sanata Maidoki Ya Tantance Dalibai Sama Da 805 A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin bayar da tallafin karatu na Sanata Garba Musa Maidoki mai wakiltar mazabar Kebbi ta Kudu, ya biya wa jimillar dalibai sama da 805 domin samun tallafin karatu.

Biyan kudaden ya hada da dalibai 291 daga Jami’ar Aikin Gona ta Tarayya da ke Zuru (FUAZ) da kuma dalibai 514 daga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kebbi da ke Aliero (KSUSTA).

  • ‘Yan Bindiga Sun Kone Ofishin ‘Yansanda A Anambra 
  • Yaƙi Da ‘Yan Bindiga: Yadda Gwamna Dauda Ya Karɓi Baƙuncin Babban Hafsan Tsaro

Sai dai kwamitin ya gano wani dalibi da bayanan da ya bayar ba su inganta ba, wanda hakan ya sa aka sallame shi daga tantancewar.

Bisa hakan ne kwamitin Suka sallami wanda aka gano daga rashin ba su kudin tallafin karatun.

Domin ka’idar shi ne sai wanda ya nuna shaidar zama dan kananan hukumomin da suka kunshin mazubun Kebbi ta kudu, ko daga masarautar Yauri ko Zuru.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

Daliban da kwamitin ya tantance sahihincin takardun su sun karbi Naira 35,000 kowane bayan an kammala tantance su.

Shugaban kwamitin, Farfesa Umar Ahmad Sanda, ya bayyana jin dadinsa da aikin, inda ya yaba wa ‘yan kwamitin bisa kwazon da suka yi.

Farfesa ya bayyana cewa takardun da ake bukata sun hada da takardar zama dan asalin karamar hukuma, katin shaidar zama dan kasa, ba da izinin shiga jami’a, da katin shaidar zama ɗalibi a jami’a.

Dalibin da aka hana ya yi ikirarin cewa daga karamar hukumar Yauri ya fito amma takardun da aka gabatar sun nuna cewa mallakar karamar hukumar Birnin Kebbi ce.

Shugaban kwamitin ya bukaci dalibai da su yi watsi da kansu idan ba su da takardun da ake bukata, yana mai gargadin cewa bincike zai gano duk wanda bai da bayanan da suka dace.

Ya kuma yaba da goyon bayan da ‘yan kwamitin, shugabannin jami’a, da kuma Sanata Maidoki suka samu a bisa jajircewarsa na karfafa wa matasa musamman masu karatu a jami’o’in kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaiKebbiSanataTallafin Karatu
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kone Ofishin ‘Yansanda A Anambra 

Next Post

An Masa Daurin Watanni 4 Kan Satar iPhone Guda 2

Related

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

1 hour ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

4 hours ago
Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi
Labarai

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

6 hours ago
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
Labarai

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

8 hours ago
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Labarai

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

9 hours ago
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya
Manyan Labarai

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Mijina Ya Sa Min Magani A Gado Don Ya Kashe Ni –Matar Aure

An Masa Daurin Watanni 4 Kan Satar iPhone Guda 2

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

June 23, 2025
Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

June 23, 2025
Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

June 23, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

June 23, 2025
Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

June 23, 2025
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

June 23, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya

June 23, 2025
Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya

June 23, 2025
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

June 23, 2025
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.