• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwanturolan Kwastam Ya Yanke Jiki Ya Fadi A Filin Jirgin Saman Kano, Ya Rasu 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kwanturolan Kwastam Ya Yanke Jiki Ya Fadi A Filin Jirgin Saman Kano, Ya Rasu 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanturolan da ke kula da Sashen Kasuwanci na Hukumar Kwastam ta Nijeriya, Anthony Ayalogu, ya rasu. 

An ce Ayalogu ya fara rashin lafiya a filin jirgin saman Malam Aminu Kano a ranar Litinin.

  • Muna Kan Kokarin Magance Matsalar Hauhawar Farashin Kayan Masarufi —Buhari
  • Ambaliyar Ruwa: Gwamnan Bayelsa Ya Ayyana Hutun Kwanaki 7 Ga Ma’aikata 

Rahotanni sun bayyana cewa shugaban na Kwastam din ya fita hayyacinsa, inda aka garzaya da shi Asibitin Sojojin Sama da ke Kano, inda aka tabbatar da rasuwarsa da misalin karfe 8:20 na daren jiya.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, AA Maiwada na sashin hulda da jama’a na NCS, ya ce, “Ya na kan hanyar zuwa wani aiki a hukumance, sai ya fara rashin lafiya da ya isa filin jirgin sama na Malam Aminu Kano, sai ya fita hayyacinsa. Duk kokarin da aka yi na ba shi kulawa ya ci tura domin ya rasu ne a ranar Litinin 17 ga Oktoba, 2022 a Asibitin Sojin Sama na Nijeriya 465 da ke Kano.

Ya kasance yana da shekaru 57.” Dan asalin karamar hukumar Onitsha ta Arewa da ke Jihar Anambra ne, Ayalogu ya yi karatun digiri na farko a fannin Botany a Jami’ar Fatakwal.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Ya shiga aikin Kwastam a ranar 24 ga Satumba, 1991 a matsayin Mataimakin Sufurtanda na Kadet.

Shugaban Hukumar Kwastam, Kanal Hameed Ali (mai ritaya), ya jajanta wa ‘yan uwa da abokan arziki na marigayi Ayalogu, inda ya ce za a yi kewarsa matuka.

“Muna addu’ar Allah ya bai wa iyalan Ayalogu kwarin guiwar jure wannan rashi nasu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Filin Jirgin SamakanoKwanturolaKwastamRashin LafiyaRasuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin Fili Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 2 A Neja

Next Post

Dan Shekara Hudu Ya Kubuta Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Yobe

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

15 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

19 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

20 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

2 days ago
Next Post
‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Kwato Makamai 

Dan Shekara Hudu Ya Kubuta Daga Hannun 'Yan Bindiga A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Zasu Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.