• English
  • Business News
Saturday, June 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyan Alkawari Cikawa

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kyan Alkawari Cikawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akwai wasu mutane 2, daya ya iya magana sosai, amma ya kan manta da maganar da ya fada, yayin da dayan ba ya son magana, sai dai duk wani alkawari da ya yi, zai yi kokarin cika shi.

A cikin mutanen nan 2 wanne ka fi so? Tabbas za a kulla abota tare da mutum na biyu ko? Saboda “Alkawari kaya ne”. Ba za a iya dogaro kan wani ba, idan ba zai iya cika alkawari ba.

  • Nasarorin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka A Shekaru Goman Baya

Wani babban dalilin da ya sa kasar Sin ta zama aminiyar kasashen Afirka, shi ne yadda suke iya dogaro da ita, wato yadda take kokarin cika alkawarin da ta yi.

Don tabbatar da gaskiyar maganar, za mu iya kwatanta alkawarin da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi, a taron ministocin dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) da ya gudana a birnin Dakar na Senegal, a karshen shekarar 2021, da jawabin da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi, wajen taron jami’ai masu kula da aiwatar da sakamakon taron ministoci na FOCAC, wanda ya gudana a kwanan baya, inda jami’in ya yi bayani kan yadda kasar Sin take kokarin cika alkawarinta.

A wajen taron Dakar, shugaba Xi ya ce kasar Sin za ta ba kamfanonin hada-hadar kudi na kasashen Afirka lamuni, na cin bashin da ya kai dala biliyan 10 cikin shekaru 3 masu zuwa.

Labarai Masu Nasaba

Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

Zuwa yanzu watanni 8 sun wuce, an riga an ba da lamuni na samun bashin da ya kai dala biliyan 3. Ban da haka, kasar Sin ta ba da rance na dala biliyan 2.5, don tallafawa kokarin gudanar da wasu manyan ayyuka a kasashen Afirka.

A taron da ya gudana a bara, shugaba Xi ya ce kasar Sin za ta yi kokarin shigo da kayayyakin kirar kasashen Afirka da darajarsu za ta kai dala biliyan 300 cikin shekaru 3. Sa’an nan cikin watanni 7 da suka wuce, kasar Sin ta riga ta shigo da kayayyaki na dala biliyan 70.6 daga Afirka.

Yayin da a nasu bangare, kamfanonin Sin sun zuba jari da ya kai dala biliyan 2.17 ga kasuwannin kasashen Afirka, cikin watanni fiye da 8 da suka gabata.

A fannin aikin kiwon lafiya, shugaba Xi ya ce cikin shekaru 3, kasar Sin za ta ba da tallafin alluran rigakafin cutar COVID-19 miliyan 600 ga kasashen Afirka, haka kuma kamfanonin kasar da na kasashen Afirka, za su yi hadin gwiwa wajen samar da alluran rigakafin cutar COVID-19 miliyan 400.

Zuwa yanzu, wasu watanni 8 sun shude, kasar Sin ta riga ta ba da tallafin alluran rigakafin cutar COVID-19 miliyan 189 ga wasu kasashe 27 dake nahiyar Afirka, kana kamfanonin kasar ta yi kokarin hadin kai tare da takwarorinsu dake kasashen Afirka wajen sarrafa alluran, inda karfinsu ya kai samar da alluran rigakafi kimanin miliyan 400 a duk shekara.

Sauran ayyukan tallafi da hadin gwiwa da kasar Sin ta yi alkawarin aiwatar da su a kashen Afirka, sun hada da gina babban ginin hedkwatar cibiyar kandagarkin cututtuka ta nahiyar Afirka, da sauran manyan asibitocin hadin gwiwa, da rage talauci, da raya bangaren makamashi mai tsabta, da aikin tsaro, da dai sauransu, duk ana kokarin ciyar da su gaba, kamar yadda kasar Sin ta yi alkawari a baya.

Me ya sa kasar Sin take dora matukar muhimmanci kan cika alkawari? Saboda babbar manufar kasar Sin ta fuskar hadin gwiwa da kasashen Afirka ita ce, “gaskiya, da daukar takamaiman matakai, da zumunta, da sahihanci”, gami da “dora muimmanci kan adalci maimakon moriya”.

Kana Sin ta tsara wannan manufa ce bisa tushen akidarta ta “al’ummar dan Adam mai makomar bai daya”.

A ganin Sinawa, dole ne a yi kokarin tabbatar da ci gaban harkoki a kasashe daban daban, kafin a iya tabbatar da makomar bai daya mai haske ta daukacin dan Adam.

Wannan akida ta sa kasar Sin ke nuna cikakken sahihanci ga kasashen Afirka, da kokarin cika alkawarinta, yayin da take hulda da su. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Karon Farko Gwamnatin Kano Za Ta Nada Matashi Mai Karancin Shekaru Mukamin Kwamishina

Next Post

Girmama Cikakken ’Yanci Da Yankunan Kasa, Wajibi Ne A Kan Kowacce Kasa Babba, Ko Karama

Related

Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 
Daga Birnin Sin

Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

15 hours ago
Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

16 hours ago
Sin Ta Jadadda Wajibcin Daukar Jerin Matakan Magance Matsalar Talauci Da Karancin Ci Gaba Da Rikici
Daga Birnin Sin

Sin Ta Jadadda Wajibcin Daukar Jerin Matakan Magance Matsalar Talauci Da Karancin Ci Gaba Da Rikici

18 hours ago
Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya
Daga Birnin Sin

Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya

19 hours ago
Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba
Daga Birnin Sin

Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

20 hours ago
An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana

21 hours ago
Next Post
Girmama Cikakken ’Yanci Da Yankunan Kasa, Wajibi Ne A Kan Kowacce Kasa Babba, Ko Karama

Girmama Cikakken ’Yanci Da Yankunan Kasa, Wajibi Ne A Kan Kowacce Kasa Babba, Ko Karama

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 

June 21, 2025
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

June 21, 2025
Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano

Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano

June 21, 2025
Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa

Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa

June 21, 2025
Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa

Za Mu Tabbatar Da Yin Aiki Da Ƙungiyar Mahaddata Alƙur’ani – Daurawa

June 21, 2025
Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata

Hajjin Bana: Jihohi 11 Sun Kashe Naira Biliyan 6.2 Kan Mahajjata

June 21, 2025
Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC Faɗuwa A 2027 – Aminu Boyi 

Wanda Ya Yi Gangancin Taba Takarar Shettima Ya Gayyato Wa APC Faɗuwa A 2027 – Aminu Boyi 

June 21, 2025
Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje

Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje

June 21, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Duk Da Jihohin Nijeriya Sun Fara Biyan Mafi Ƙarancin Albashi Na 70,000, Ana Ci Gaba Da Fuskantar Matsin Rayuwa

June 21, 2025
Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

June 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.