• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
1 year ago
Inec

A yayin da zaben gwamnan Jihar Edo ke kara gabatowa, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta bayyana laifukan zabe a matsayin daya daga cikin manyan barazana ga samun sahihan zabuka a Nijeriya.

 

An bayyana cewa hukumar ta lura cewa laifukan zabe na kara tayar da hankali a siyasance da haifar da tarzoma a cikin kasar nan.

  • Kotu Ta Umarci INEC Ta Tuhumi Gwamnoni Kan Rikice-rikicen Zaben 2023
  • Tinubu Ya Amince Da Karin Albashi Da Kashi 300 Ga Alkalan Nijeriya

Shugabar sashen shari’a na ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) reshen Jihar Edo, Mrs Rita Amadi ta bayyana hakan a wata takarda da ta gabatar a wani taron yini daya da kungiyoyin matasa a Jihar Edo kan rawar da matasa za su taka gabanin zaben gwamna a ranar 21 ga Satumba, 2024.

 

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Amadi, wacce jami’in shari’a a ofishin Benin, Misis Oba Agbonifo ta wakilta, a takardarta mai suna, ‘Laifukan zabe da hukunce-hukuncensa’, ta ce makasudin gabatar da taron shi ne, a wayar da kan jama’a, musamman matasa game da dokokin zabe da kuma hukuncin da doka ta tanada ga duk wanda ya karya dokokin zabe.

 

Ta yi nuni da cewa gurfanar da wadanda suka aikata laifukan zabe a Nijeriya ya zama babban aiki. A cewarta, daya daga cikin manya-manyan matsalolin da ke hana gudanar da sahihin shari’a kan laifukan zabe shi ne, rashin ingancin binciken laifuka a Nijeriya.

 

Amadi ta bayyana cewa kokarin rage laifukan zabe zai iya yin tasiri ne kawai ta hanyar kamawa, gurfanar da masu laifi da kuma hukuntasu, domin nuna izina ga masu sha’awar aikata laifi.

 

“Mutum ko gungun mutane na iya aikata laifukan zabe, kuma ya kamata irin wadannan mutane su fuskanci hukunci daidai da dokokin zabe da kasa ta tanada.

 

“Dokokinmu sun tanadi hukunci ga wadanda suka aikata laifukan zabe. Bugu da kari, matasa sun fi yawa a cikin al’ummarmu, sannan sun fi yawa ga mutanen da ke shiga harkar zabenmu a matakai daban-daban.

 

“A kan wannan yanayin yana da matukar muhimmanci matasa su fahimci laifukan zaben,” in ji ta.

 

Jami’ar shari’a ta INEC ta ce shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai, inda ya ce duk da cewa hukumar zabe ta ba ta ikon hukunta wadanda suka aikata laifukan zabe tare da rashin ikon da za su bayar wajen kamawa da kuma binciki laifukan zabe “.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan ‘Yancin Kananan Hukumomi – PDP

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.