• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC

by Sulaiman and Yusuf Shuaibu
11 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Inec
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da zaben gwamnan Jihar Edo ke kara gabatowa, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta bayyana laifukan zabe a matsayin daya daga cikin manyan barazana ga samun sahihan zabuka a Nijeriya.

 

An bayyana cewa hukumar ta lura cewa laifukan zabe na kara tayar da hankali a siyasance da haifar da tarzoma a cikin kasar nan.

  • Kotu Ta Umarci INEC Ta Tuhumi Gwamnoni Kan Rikice-rikicen Zaben 2023
  • Tinubu Ya Amince Da Karin Albashi Da Kashi 300 Ga Alkalan Nijeriya

Shugabar sashen shari’a na ofishin hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) reshen Jihar Edo, Mrs Rita Amadi ta bayyana hakan a wata takarda da ta gabatar a wani taron yini daya da kungiyoyin matasa a Jihar Edo kan rawar da matasa za su taka gabanin zaben gwamna a ranar 21 ga Satumba, 2024.

 

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Amadi, wacce jami’in shari’a a ofishin Benin, Misis Oba Agbonifo ta wakilta, a takardarta mai suna, ‘Laifukan zabe da hukunce-hukuncensa’, ta ce makasudin gabatar da taron shi ne, a wayar da kan jama’a, musamman matasa game da dokokin zabe da kuma hukuncin da doka ta tanada ga duk wanda ya karya dokokin zabe.

 

Ta yi nuni da cewa gurfanar da wadanda suka aikata laifukan zabe a Nijeriya ya zama babban aiki. A cewarta, daya daga cikin manya-manyan matsalolin da ke hana gudanar da sahihin shari’a kan laifukan zabe shi ne, rashin ingancin binciken laifuka a Nijeriya.

 

Amadi ta bayyana cewa kokarin rage laifukan zabe zai iya yin tasiri ne kawai ta hanyar kamawa, gurfanar da masu laifi da kuma hukuntasu, domin nuna izina ga masu sha’awar aikata laifi.

 

“Mutum ko gungun mutane na iya aikata laifukan zabe, kuma ya kamata irin wadannan mutane su fuskanci hukunci daidai da dokokin zabe da kasa ta tanada.

 

“Dokokinmu sun tanadi hukunci ga wadanda suka aikata laifukan zabe. Bugu da kari, matasa sun fi yawa a cikin al’ummarmu, sannan sun fi yawa ga mutanen da ke shiga harkar zabenmu a matakai daban-daban.

 

“A kan wannan yanayin yana da matukar muhimmanci matasa su fahimci laifukan zaben,” in ji ta.

 

Jami’ar shari’a ta INEC ta ce shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai, inda ya ce duk da cewa hukumar zabe ta ba ta ikon hukunta wadanda suka aikata laifukan zabe tare da rashin ikon da za su bayar wajen kamawa da kuma binciki laifukan zabe “.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Na Yi Mamakin Ganin Takardar Tuɓe Rawanina Na Sarautar Mujaddadin Bauchi – Sanata Buba

Next Post

Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan ‘Yancin Kananan Hukumomi – PDP

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

Har Yanzu Tsugune Ba Ta Kare Ba Kan ‘Yancin Kananan Hukumomi – PDP

LABARAI MASU NASABA

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.