Abba Ibrahim Wada">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

Laporta Ya Zargi PSG Da Jefa Barcelona Rudani

by Abba Ibrahim Wada
January 28, 2021
in WASANNI
1 min read
Laporta Ya Zargi PSG Da Jefa Barcelona Rudani
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Dan takarar shugabancin kungiyar kwallon kafa ta Barcelona wanda shine ake ganin zai lashe zaben, Joan Laporta, ya zargi kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint German da haddasawa kungiyar rudani, sakamakon soma tuntubar kaftin dinsu Lionel Messi.

A makon jiya daraktan wasannin kungiyar PSG, Leonardo ya ce kulla yarjejeniya da manyan ‘yan wasa irinsu Messi shi ne burinsu, yayin da kuma a farkon makon nan, dan wasan tsakiya na kungiyar ta PSG Leandro Paredes ya ce tuni suka soma tuntubar kaftin din na Barcelona don haka a yanzu wuka da nama na hannunsa.
A karshen kakar wasa ta bana yarjejeniyar Messi da Barcelona za ta kare, bayan kokarin katse ta da dan wasan yayi a shekarar bara, abinda ya janyo kai ruwa rana tsakaninsa da kungiyar wanda har yayi sanadiyar tafiya da kujerar shugaban kungiyar Jose Maria Bartemeu.
Tun a kakar wasa ta bara ne kuma ake alakanta Messi da komawa kungiyar PSG ko kuma Manchester City, kungiyar da a waccan lokacin har ta tattauna da maihafin tauraron na dan wasan.
Itama kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ta tattauna da mahaifin dan wasan wanda daga baya ya bayyana cewa dan nasa zai cigaba da zaman kungiyar har zuwa karshen kakar wasa ta bana wadda za ta kare a watan Mayun bana.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Rashin Kudi Yana Neman Saka Real Madrid Hakura Da Mbappe

Next Post

Zan Taimaka Wa Arsenal Wajen Samun Tikitin Kofin Zakarun Turai – Odegard

RelatedPosts

PSG

Bambancin Tuchel Da Pochettino A PSG

by Abba Ibrahim Wada
22 hours ago
0

Ranar Lahadi kungiyar kwallon kafa ta Monaco ta je har...

Kallo

’Yan Kallo Za Su Koma Shiga Kallo A Watan Mayu A Ingila

by Abba Ibrahim Wada
1 day ago
0

Kimanin 'yan kallon kwallon kafa 10,000 za su koma shiga...

Yadda Aka Raba Jadawalin Kofin Zakarun Afrika

by Abba Ibrahim Wada
1 day ago
0

An hada kungiyoyi uku da suka taba lashe kofin zakarun...

Next Post
Zan Taimaka Wa Arsenal Wajen Samun Tikitin Kofin Zakarun Turai – Odegard

Zan Taimaka Wa Arsenal Wajen Samun Tikitin Kofin Zakarun Turai – Odegard

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version