Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home NOMA

Legas Ba Za Ta Ci  Gaba Da Dogaro Da Arewa Wajen Samun Abinci Ba – Gwamnatin Jihar

by Muhammad
April 7, 2021
in NOMA
2 min read
Abinci
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba,

Gwamnatin jihar Legas ta shelanta cewa tana yin dubi wajen habaka noma a jihar domin  ba za ci  gaba da yin dogaro kan jihohin Arewacin kasar nan  domin samar da wadataccen abinci a jihar ba.

In za a iya tuna wa,  Gwamnatin na mayar da martani ne kan dakatar da kai abinci  zuwa Kudancin kasar nan daga Arewacin Nijeriya da gamaiyyar kungiyoyin safarar abinci da kuma dabbobi suka yi a kwanan baya, inda hakan ya janyo tashin farashin abincin  da kuma dabbobi.

Kwamishiniyar  ma’aikatar aikin gona ta jihar  Abisola Olusanya ce ta shelanta hakan  a taron bayar da horo na kwana biyar ga malaman gona da ya gudana a jihar.

Taron wanda aka gudanar dashi a jihar ta Legas, Hukumar Bunkasa  Aikin Gona  (LSADA) tare da hadin gwiwa da ma’aikatar aikin gona da raya karkara ta jihar ce suka shirya shi.

Bugu da kari,  manufar bayar da horon shi ne a karfafa wa malam gona kwarin gwiwa  da kuma ilimantar da su kan yin aikin noma na zamani,  inda alfanun zai koma kan manoman dake a jihar,  musamman domin kara bunkasa samar da wadataccen abinci a jihar.

A cewar Kwamishiniyar ta  ma’aikatar aikin gona ta jihar  Abisola Olusanya,  Legas ba za ta ci gaba da dogaro  kan Arwacin Nijeriya ba wajen samun wadataccen abinci.

Kwamishiniyar  ma’aikatar aikin gona ta jihar  Abisola Olusanya ya ci gaba da da cewa, wannan  abu ne dan lokaci,  inda ta kara da cewa,  hakan ne ya zaburar da Gwamnatin jihar wajen bai wa malam gona horo.

Kwamishiniyar  ta bayyana cewa, samun malaman da za su gudanar da hakan,  ya zama dole a a karfafa masu gwiwa,  inda kuma ta bukaci da a kara samar masu da dauki .

Abisola Olusanya ta ci gaba da cewa, “A matsayin ku na malaman gona,  ba wai ana bukatar ku koya wa manoman aikin noma na zamani ba kawai  ya kuma zama wajibi ku ilmantar da manoman kan yadda amfanin gonar da suka noma su samu farashi mai kyau a kasuwa”.

Ta sanar da cewa, har ila yau hakan na nuna za ku koya wa manoman kasuwancin noma, musamman domin su samu kudin shiga masu yawa.

Abisola Olusanya  ga su malam gonar,  ya zama dole a ba ku kwarin gwiwa kan aikin da za ku gudanar da kuma samar masu da dauki.

Kwamishiniyar ma’aikatar aikin gonar ta ce, na lura da cewa,  muna fuskantar karancin malaman aikin gona a jihar Legas,  amma za mu kara zage damtse don kara samar da malaman da dama,  musamman kan yunkurin da gwamnatun jihar ke kan yi na habaka aikin nomaa jihar da kuma yin amfani da fannin wajen kara bunkasa tattalin arzikin jihar da da kuma kara wadata jihar da abinci mai yawa da da kuma kasa baki daya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Juventus Ta Shirya Rabuwa Da Ronaldo

Next Post

Nijeriya Da Sudan Da Chadi Suka Fi Fitar Da Karo Zuwa Ketare, Cewar Rahoton UNCTAD

RelatedPosts

Noma

Aikin Noma Na APPEALS Ya Kawo Ci Gaba A Legas -Manoma

by Muhammad
7 hours ago
0

Daga Abubakar Abba, Fannin aikin noma ako wacce kasa na...

Masara

Batun Masana’antun Kiwon Kajin Da Daukin CBN Na Samar Da Tan 300,000 Na Masara

by Muhammad
7 hours ago
0

Daga Abubakar Abba, A kimanin watanni sha biyar da suka...

Har Yanzu Nijeriya Na Shigo Da Madara Kashi 60 Cikin Dari – Nanono

Har Yanzu Nijeriya Na Shigo Da Madara Kashi 60 Cikin Dari – Nanono

by Sulaiman Ibrahim
6 days ago
0

Daga Abubakar Abba Ministan ma’aikatar aikin gona da raya karkara...

Next Post
Karo

Nijeriya Da Sudan Da Chadi Suka Fi Fitar Da Karo Zuwa Ketare, Cewar Rahoton UNCTAD

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version