• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Legas Ta Laƙume Aikin Naira Tiriliyan 3.9 Cikin Shekaru Biyun Tinubu

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
in Manyan Labarai
0
Legas Ta Laƙume Aikin Naira Tiriliyan 3.9 Cikin Shekaru Biyun Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rahoton Daily Trust ya bayyana cewa a cikin shekaru biyu na mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, jihar Legas ta samu amincewar ayyuka daga gwamnatin tarayya da suka kai darajar Naira tiriliyan 3.9, adadin da ya fi gaba ɗaya abin da aka ware wa jihohin Arewa maso Yamma, Arewa maso Gabas da kuma Kudu maso Gabas. Wannan ya tayar da cece-kuce kan batun adalci da daidaituwar raba kuɗaɗen ci gaban ƙasa.

Binciken ya nuna babban giɓin da ke cikin rabon kasafin ayyukan ci gaba a Nijeriya. Duk da cewa Legas kaɗai ta samu ayyuka da darajar tiriliyan 3.9, jihohin Kudu maso Gabas (N407.49bn), Arewa maso Yamma (N2.7trn), da Arewa maso Gabas (N403.98bn) sun raba jimillar tiriliyan 3.56. Yankin Kudu maso Yamma, wanda Legas ke ciki, ya fi kowa samu da jimillar tiriliyan 5.97, da suka haɗa manyan ayyuka irin su Lagos-Calabar Coastal Highway da gyaran filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ya kai Naira biliyan 712.

  • ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
  • ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

Sai dai gwamnatin tarayya ta ƙaryata zargin nuna bambanci. Ministan yaɗa labarai Mohammed Idris, ya bayyana cewa shirin Renewed Hope Agenda na Tinubu yana tafiya bisa tsarin adalci, inda ya nuna ayyuka irin su hanyar Sokoto-Badagry da jiragen ƙasa a Kano da Kaduna a matsayin hujja na aikin “ci gaban ƙasa baki ɗaya.”

Amma masu suka na ganin lambobin sun tabbatar da akasin hakan. Wani Jigon PDP, Timothy Osadolor, ya zargi Shugaban ƙasa da yin mulkin ƙabilanci fiye da na ƙasa baki ɗaya, yana mai cewa sauran yankuna suna samun “ragowar ci gaba.” Haka kuma, mai fafutukar kare haƙƙin ɗan adam, Auwal Rafsanjani, ya soki doka da tsarin kashe makudan kuɗaɗe ba tare da tsayayyen kasafi ba, yana mai danganta matsalar da “tsarin da ke tsotsar gumin wasu” wanda ke haddasa rashin ci gaba da jin cewa ana nuna wariya.

Wannan bincike ya sake fito da tsohon ƙalubale a tsarin mulkin Nijeriya: yadda za a daidaita muhimmancin raya cibiyoyin tattalin arziƙi irin su Legas da kuma wajabcin adalci wajen rabon arzikin ƙasa.

Labarai Masu Nasaba

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Yayin da gwamnatin Tinubu ke ci gaba da tura manyan ayyukan ci gaba zuwa Legas, tambaya a nan shi ne: shin za a ji daɗin “Renewed Hope” daidai da yadda ake ji a bakin tekun Legas a ƙauyukan Arewa maso Gabas?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

Next Post

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

Related

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

12 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

12 hours ago
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

23 hours ago
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

24 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

1 day ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

2 days ago
Next Post
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya - Kungiyar Kwadago

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Legas

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.