ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Libya Ta Ba Da Umarnin Tsare Jakadiyar Brussels Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa

by Sadiq
2 years ago
Libya

Babban mai shigar da kara na Libya ya ba da umarnin a tsare jakadiyar kasar a Brussels a ranar Talata bisa zargin cin hanci da rashawa, jim kadan bayan da gwamnatin Tripoli da kasashen duniya suka amince da sallame ta.

An yi wa Amel Jerry tambayoyi game da “cin zarafin gwamnati da na kudi” da ake zargin an yi amfani da ita don “samun fa’idar haram ta hanyar kwace dukiyar jama’a ba bisa ka’ida ba da kuma cutar da muradun jama’a”, in ji ofishin mai gabatar da kara Al-Seddik al-Sour.

  • ‘Yan Fashin Daji Sun Kashe Kansila A Katsina
  • Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Abinci

Da yake lura da “dacewar shaidar” kan jakadiyar, Al-Sour ya tuhume ta tare da ba da umarnin tsare ta na wucin gadi, in ji ofishin a cikin wata sanarwa, ba tare da bayyana inda ta ke ba.

ADVERTISEMENT

Tun da farko gwamnatin da Majalisar Dinkin Duniya ta amince da shi a yammacin Libya ta sanar da korar Jerry ba tare da bayar da wani bayani ba.

Kasar Libya mai arzikin man fetur ta fada cikin rikici tun bayan boren da mutanen kasar suka yi a 2011 wanda ya hambarar da gwamnatin shugaba Moamer Gadhafi, kuma cin hanci da rashawa ya yi kamari a cikin cibiyoyin gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

EU Ta Koka Da Yadda Yaduwar Ta’addanci A Sahel Ke Barazana Ga Tsaron Turai

Trump Ya Caccaki Kasashen Turai Bayan Ayyana Nahiyar A Matsayin Mai Rauni

Kasar da ke arewacin Afirka ta kasance cikin rarrabuwar kawuna tsakanin gwamnatoci biyu masu gaba da juna, daya a Tripoli da kuma daya a gabashin Libya da ke samun goyon bayan wani babban soji Khalifa Haftar.

Batun cin hanci da rashawa na baya-bayan nan ya barke ne bayan da aka yada wani faifan murya da aka danganta shi da Jerry a shafukan sada zumunta.

A cikin faifan bidiyon, ana iya jin wata mace tana magana wadda aka bayyana a matsayin sakatariyarta, tana mai da’awar cewa tana bukatar “rasitan karya” na sama da Yuro 200,000 (dala $209,000) don maganin cutar kansa ga wani majiyyaci na Libya.

Sakatariyar ta tabbatar da sahihancin faifan bidiyon ga kafafen yada labarai na Libya.

A cikin faifan bidiyon, matar ta ce dole ne a aika da daftarin zuwa ma’aikatar lafiya ta Libya don samun amincewarta na sakin kudaden.

Biyan kudaden jinya ga ‘yan kasar Libya a kasashen waje, daidaitacciyar al’ada ce ga wakilan kasashen duniya na Libya, amma jami’ai a kai a kai suna yin tir da rashin bin ka’ida.

A cewar jaridar Le Soir ta kasar Belgium, ana kuma zargin Jeary da “shakku” wajen mika kudaden al’ummar Libya da ya kai dubunnan daruruwan daloli, zuwa wani kamfani mallakar danta.

Rahotanni daga kasar Belgium na cewa jakadiyar ta koma kasar Libya, sai dai kawo yanzu babu tabbacin hakan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

EU Ta Koka Da Yadda Yaduwar Ta’addanci A Sahel Ke Barazana Ga Tsaron Turai
Kasashen Ketare

EU Ta Koka Da Yadda Yaduwar Ta’addanci A Sahel Ke Barazana Ga Tsaron Turai

December 14, 2025
Trump Ya Caccaki Kasashen Turai Bayan Ayyana Nahiyar A Matsayin Mai Rauni
Kasashen Ketare

Trump Ya Caccaki Kasashen Turai Bayan Ayyana Nahiyar A Matsayin Mai Rauni

December 14, 2025
Rwanda Ta Musanta Hannu A Rikicin Da Ya Barke A Kibu Da DR Congo
Kasashen Ketare

Rwanda Ta Musanta Hannu A Rikicin Da Ya Barke A Kibu Da DR Congo

December 14, 2025
Next Post
An Gurfanar Da Mutane 14 Kan Karyar Bacewar Mazakuta A Abuja

An Gurfanar Da Mutane 14 Kan Karyar Bacewar Mazakuta A Abuja

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.