• English
  • Business News
Monday, October 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Libya Ta Ba Da Umarnin Tsare Jakadiyar Brussels Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa

by Sadiq
2 years ago
in Kasashen Ketare
0
Libya Ta Ba Da Umarnin Tsare Jakadiyar Brussels Kan Zargin Cin Hanci Da Rashawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban mai shigar da kara na Libya ya ba da umarnin a tsare jakadiyar kasar a Brussels a ranar Talata bisa zargin cin hanci da rashawa, jim kadan bayan da gwamnatin Tripoli da kasashen duniya suka amince da sallame ta.

An yi wa Amel Jerry tambayoyi game da “cin zarafin gwamnati da na kudi” da ake zargin an yi amfani da ita don “samun fa’idar haram ta hanyar kwace dukiyar jama’a ba bisa ka’ida ba da kuma cutar da muradun jama’a”, in ji ofishin mai gabatar da kara Al-Seddik al-Sour.

  • ‘Yan Fashin Daji Sun Kashe Kansila A Katsina
  • Cire Tallafin Fetur: Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Abinci

Da yake lura da “dacewar shaidar” kan jakadiyar, Al-Sour ya tuhume ta tare da ba da umarnin tsare ta na wucin gadi, in ji ofishin a cikin wata sanarwa, ba tare da bayyana inda ta ke ba.

Tun da farko gwamnatin da Majalisar Dinkin Duniya ta amince da shi a yammacin Libya ta sanar da korar Jerry ba tare da bayar da wani bayani ba.

Kasar Libya mai arzikin man fetur ta fada cikin rikici tun bayan boren da mutanen kasar suka yi a 2011 wanda ya hambarar da gwamnatin shugaba Moamer Gadhafi, kuma cin hanci da rashawa ya yi kamari a cikin cibiyoyin gwamnati.

Labarai Masu Nasaba

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

Kasar da ke arewacin Afirka ta kasance cikin rarrabuwar kawuna tsakanin gwamnatoci biyu masu gaba da juna, daya a Tripoli da kuma daya a gabashin Libya da ke samun goyon bayan wani babban soji Khalifa Haftar.

Batun cin hanci da rashawa na baya-bayan nan ya barke ne bayan da aka yada wani faifan murya da aka danganta shi da Jerry a shafukan sada zumunta.

A cikin faifan bidiyon, ana iya jin wata mace tana magana wadda aka bayyana a matsayin sakatariyarta, tana mai da’awar cewa tana bukatar “rasitan karya” na sama da Yuro 200,000 (dala $209,000) don maganin cutar kansa ga wani majiyyaci na Libya.

Sakatariyar ta tabbatar da sahihancin faifan bidiyon ga kafafen yada labarai na Libya.

A cikin faifan bidiyon, matar ta ce dole ne a aika da daftarin zuwa ma’aikatar lafiya ta Libya don samun amincewarta na sakin kudaden.

Biyan kudaden jinya ga ‘yan kasar Libya a kasashen waje, daidaitacciyar al’ada ce ga wakilan kasashen duniya na Libya, amma jami’ai a kai a kai suna yin tir da rashin bin ka’ida.

A cewar jaridar Le Soir ta kasar Belgium, ana kuma zargin Jeary da “shakku” wajen mika kudaden al’ummar Libya da ya kai dubunnan daruruwan daloli, zuwa wani kamfani mallakar danta.

Rahotanni daga kasar Belgium na cewa jakadiyar ta koma kasar Libya, sai dai kawo yanzu babu tabbacin hakan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cin Hanci Da RashawaJakadiyaLibyaTsarewaZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jaruma Binta Ola Ta Rasu

Next Post

An Gurfanar Da Mutane 14 Kan Karyar Bacewar Mazakuta A Abuja

Related

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?
Kasashen Ketare

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

1 day ago
Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?
Kasashen Ketare

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

1 week ago
Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa
Kasashen Ketare

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

2 weeks ago
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya
Kasashen Ketare

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

3 weeks ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Kasashen Ketare

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

4 weeks ago
Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan
Kasashen Ketare

Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan

1 month ago
Next Post
An Gurfanar Da Mutane 14 Kan Karyar Bacewar Mazakuta A Abuja

An Gurfanar Da Mutane 14 Kan Karyar Bacewar Mazakuta A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara

October 5, 2025
Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

Kotu Ta Kori Buƙatar Ministan Tinubu Na Hana Fitar Da Takardun Karatunsa

October 5, 2025
CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

CMG Zai Watsa Shirin Nishadantarwa Na Murnar Bikin Zhongqiu Gobe Da Dare

October 5, 2025
Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

Nijeriya Ta Zamo Ƙasa Mafi Ƙarancin Tsammanin Tsawon Rayuwa A Duniya

October 5, 2025
Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridar Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.