ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

by Rabi'u Ali Indabawa
12 months ago
Sudan

Alawia Babiker Ahmed mai shekara 19 ta yi bari a lokacin da take gudu da kafa domin tsira daga kazamin yakin basasa da ya daidaita yankin Darfur na yammacin Sudan.

”Ina ta zubar da jini a kan hanya,” ta gaya wa BBC, kafin ta kara da cewa, ta ga ma mutanen da suka ma fi ta shiga tsaka-mai-wuya, wadanda yanayinsu ya fi nata a wannan lokaci da take tafiyar kwana uku ta nisan kilomita 70, cikin fargaba da tashin hankali daga birnin el-Fasher da aka yi wa kawanya zuwa dan karamin garin Tawila.

  • Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali
  • Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Alawia ta bayyana yadda ita da ‘yan’ uwanta suka ga wani dan karamin yaro yana kuka kusa da mahaifiyarsa wadda ta rasu tana yashe a gefen titi, a daidai lokacin da su kuma suke ta kauce wa hare-hare ta sama da ‘yanbindiga.

ADVERTISEMENT

Alawia ta ce ta dauki yaron, ita kuwa gawar uwar suka rufe ta, suka ci gaba da tafiya.

Sudan ta fada bala’in yakin basasa tun bayan da fada ya barke tsakanin rundunar sojin kasar da dakarun RSF, a watan Afirilu na 2023.

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

Lamarin da ya haddasa daya daga cikin bala’i da mutane suka taba fadawa, inda sama da mutum miliyan 12 suka tsere daga gidajensu.

Darfur ta kasance yankin da nan da nan rikici kan tashi, inda RSF ke iko da yawancin yankin, in banda birnin el-Fasher wanda ya ci gaba da kasancewa a hannun rundunar sojin kasar da kawayenta.

Birnin el-Fasher ya sha ruwan bama-bamai a yayin da RSF ke kokarin kama shi.

A watan Afirilu RSF din ta sanar da shirin kafa gwamnati domin zama kishiya ga gwamnatin soji, abin da ya haddasa fargaba cewa hakan zai kai ga rarraba kasar.

Alawia ta ce yayin da fadan ya tsananta ake ta ruwan bama-bamai a watan da ya gabata, dole ita da mutanen gidansu suka tsere a kafa zuwa Tawila da ke yamma da el-Fasher.

‘Ya’yanta Marwan Mohamed Adam, mai shekara 21, ya gaya wa BBC cewa mayakan da ke da alaka da RSF sun ci zarafinsa a hanya inda suka lallasa shi da duka, har suka yi masa fashin ‘yan abubuwan da yake dauke da su.

Marwan ya ce ya tsira daga hannun gungun ne saboda ya yi musu karya daga inda ya fito.

Ya ce maharan sun debe matasan da suka gaya musu cewa daga el-Fasher suke suka je suka harbe su.

”Saboda haka a lokacin da suke yi min tambayoyi na ce musu daga Shakra nake – wanda zango ne a kan hanyar zuwa Tawila,” in ji shi.

“Za ka ji tsoro da fargaba, kana cikin tashin hankali, ka ji kamar ma ka riga ka mutu,” in ji Marwan mai shekara 21, a hirarsa da BBC, inda ya kara da cewa ya ga gawawwaki uku a kan hanya.

Wata matar, Khadija Ismail Ali, ta gaya wa BBC cewa “ga gawawwaki nan yashe a titi.”

Ta ce an kashe mutum 11 ‘yan gidansu a lokacin da ake yi wa el-Fasher ruwan makamai ta sama, kuma kananan yara uku sun mutum a lokacin tattakin da suka yi na kwana hudu daga birnin zuwa Tawila.

“Yaran sun rasu ne sakamakon kishirwa a hanya,” in ji Khadija.

‘Yanbindiga masu alaka da dakarun RSF sun kai hari kan kauyen iyalinta, el-Tarkuniya, a watan Satumba da ya wuce, inda kuma suka sace musu amfanin gona.

A lokacin suka tsere zuwa sansanin Zamzam inda ake fama da yunwa, daga nan kuma suka kara gaba zuwa el-Fasher yanzu kuma zuwa Tawila.

Kungiyar bayar da agajin lafiya – Alima ta ce ‘yanbindiga sun kwace filaye da gonakin yawancin iyalai a lokacin da suka kai musu hari.

Kungiyar ta kara da cewa wadanda suke zuwa Tawila, yawanci yara tuni sun kamu da cutar tsananin yunwa.

Alawia ta ce ‘yar uwarta ta jefar da dan abincin da suka yi guziri a lokacin da suke neman tsira daga hare-haren sama da suka gamu da su bayan sun wuce Shakra.

“Dan wani guntun wake ne da ya rage da dan gishiri muka rike a hannunmu domin ciyar da yara,” ta ce. Haka suke ta tattaki ba tare da ruwa ko abinci ba, har suka hadu da wata mata da ta ce musu za su iya samun ruwa a wani kauye da ke kusa.

Tawagar tasu ta tashi cikin dare domin ci gaba da tafiya zuwa wannan kauye, to amma ba su san cewa ashe suna yanki ne da ke karkashin ikon mayakan RSF ba.

“Mun gaishe su, amma kuma ba su amsa mana ba. Sun umarce mu, mu zauna a kasa, suka bincike kayanmu,” in ji Alawia.

Mayakan sun karbe kudin da muke rike da su fan 20,000 (na Sudan) (daidai da Dala 33), gaba daya kudin da iyalan ke da shi, tare da tufafi da takalman da suke dauke da su.

“Takalmana ba su da kyau amma duk da haka suka kwace su,” in ji Alawia.

Ta kara da cewa mayakan RSF sun ki su ba su ruwa, saboda haka suka ci gaba da tafiya har sai da suka kai kauyen el-Koweim.

A can suka hangi wata rijiya da mayakan RSF ke tsare da ita.

“Mun roke su, su ba mu ruwa akalla ko don yaron nan maraya, amma suka ki,” in ji Alawia.

Ta kara da cewa ta matsa domin ta je rijiyar amma mayakan suka mangare ta.

Iyalan sun ci gaba da tafiya haka a galabaice cikin kishirwa har sai da suka kai Tawila, inda isar su ke da wuya sai Alawia ta zube kasa, nan da nan aka garzaya da iya asibiti.

An sallame ta bayan an yi mata magani.

Haka shi ma yayanta Marwan an yi masa maganin raunukan da ya ji a lokacin da mayakan suka yi masa duka.

Alawia ta ce daga nan ne suka shiga neman dangin wannan yaron da suka ceto, bayan sun same su, suka danka musu shi.

A yanzu Alawia da iyalanta na zaune a Tawila, inda wasu iyalai suka karbe su, suka ba su masauki a gidansu.

“Yanzu dai rayuwa mun gode wa Allah, amma muna da fargabar yadda za ta iya kasancew

a a nan gaba,” Alawia ta shaida wa BBC.

Sudan
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Next Post
Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Jamie Gittens Daga Borussia Dortmund

Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Jamie Gittens Daga Borussia Dortmund

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.