• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatar Sarrafa Kwakwa A Nijeriya Na Bukatar Wutar Lantarki -Dapo

by Abubakar Abba
3 years ago
Kwakwa

Aikin hukumar bunkasa noman kwakwa ta Legas ce ta taimaka wajen bunkasa harkar ta yadda za a dinga samar da ita sosai ga kasuwa.

Shugaban hukumar Dapo Olakulehin ya ce jihar ita ce kan gaba wajen samar da kwakwa a kasar nan, inda ya kara da cewa, amma ba a iya wadata kasar da ita saboda karuwar masu sarrafa ta a cikin shekara 10 zuwa 15 da suka wuce.

  • Tubabbun ‘Yan Boko Haram Sun Gudanar Da Aikin Tsabtace Muhalli A Maiduguri
  • “Korar Fulani A Edo: Ina Ake So Wadanda Aka Haifa A Jihar Shekara 50 Su Koma?”

Olakulehin ya ci gaba da cewa, a shekara uku da suka wuce, lokacin da muka ga alamar karuwar bukatarta, sai muka dinga karfafa wa mutane gwiwa kan su shiga harkar domin samar da ita yadda ake bukata.

A shekara hudu zuwa biyar masu zuwa za a fara ganin tasirin hakan idan bishiyoyin suka fara ‘ya’ya, inda ya ce hukumar bunkasa noman kwakwar ta Legas tana da fili, inda take samar da dashen itaciyar da take raba wa jama’a.

Shugaban ci gaba da cewa, a bara ta raba wa manoma har dashe dubu 200 kyauta, amma duk da haka ba su isa ba, inda ya sanar da cewa, a bana kuwa dashe dubu 80 kawai hukumar ta iya raba wa, wanda wannan na nufin masu sarrafa kwakwar a Nijeriya dole ne su ci gaba da sayo ta daga waje kafin wani lokaci nan gaba.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

Shi kuwa wani babban jami’i a Ma’aikatar Masana’antu da kasuwanci da zuba jari ta kasa Kaura Arimiye, cewa ya yi gwamnati ta dauki wannan harka a matsayin wata hanya ta rage yawan marasa aikin yi da kuma rage dogaron da kasar ke yi a kan man fetur domin samun kudi daga kasar waje.

Wata mai kamfanin sarrafa kwakwar, wajen yin abubuwa daban-daban Ebun Feludu, ta ce, tana ganin idan gwamnati na son cim ma bukatar hakan to sai ta bunkasa muhimman abubuwan inganta rayuwa kamar wutar lantarki da tituna da sauransu.

Ta ce Nijeriya ta yi kaurin suna wajen rashin wutar lantarki, haka ma tituna ba su da kyau, inda ta kara da cewa, akwai bukatar gwamnatin ta rage hidima da kudin fitar da kayan zuwa kasuwannin duniya.

Shugabar kungiyar manoma da masu sarrafawa da sayar da kwakwar na kasa Nma Okoroji, ta ce mutane na kara samun wayewa da fahimtar cewa harka ce ta samun kudi.

Nma ta ci gaba da cewa, kwakwa za ta iya kara yawan kudin da Nijeriya ke samu, inda ta bayyana cewa, muna da kyakkyawan yanayi da filin nomanta da kuma manoman, da su yi ta.

Ta ce, muna ma fitar da ita kasashe maimakon mu sayo daga ketare, inda ta kara da cewa, mutane da yawa a Afirka ta Yamma na ci da shan ruwan kwakwa.

Ta kara da cewa , aiki karkashin wani shiri na bunkasa samar da kwakwar a kasar nan, tare da tallafin gwamnati, inda ta sanar da cewa, shirin da a karkashinsa ake kudurin dasa itatuwan kwakwa a fili mai girman hekta 10,000 a yawancin jihohin Nijeriya 36 zuwa shekara ta 2027.

Ta sanar da cewa, sai dai babbar matsalar ita ce ta samun ingantaccen irin kwakwar, inda ta ci gaba da cewa, iri ma fi inganci shi ne na aure wanda aka samar daga, hadin doguwar bishiyar kwakwar ta Afirka ta Yamma da kuma gajeruwa ta yankin Asiya.

Ta bayyana cewa, shekara hudu zuwa biyar, ba kamar gajeruwa ta Asia ba, wadda take fara ‘ya’ya a cikin shekara biyu da rabi zuwa uku, inda ta ce amma kuma ita ta aure kwararru sun samar da ita ne musamman domin noma na kasuwanci.

Shi ma wani da ke a cikin fannin mai suna Abiodun Oyelekan, ya ce yana da kyau a yi amfani da kwakwar ‘yar aure saboda yawan ‘ya’yan da take samarwa a shekara.

Ya sanar da cewa, amma tana da tsada domin duk dashe daya ya kai kusan dala shida wanda hakan ya sa ta fi karfin yawancin kananan manoman da ke a cikin fannin a kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
RTEAN Za Ta Jagoranci Samar Da Motoci Masu Amfani Da Iskar Gas A Nijeriya

RTEAN Za Ta Jagoranci Samar Da Motoci Masu Amfani Da Iskar Gas A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci

Shugaban NAHCON Ya Musanta Zargin Tsare Ɗan Jarida Da Aikata Cin Hanci

October 22, 2025
Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars

October 22, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

Rashin Abinci Mai Gina Jiki Barazana Ce Ga Lafiyar Al’umma – Gwamna Lawal

October 22, 2025
Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

Majalisa Ta Amince Da Dokar Ɗaurin Rai Da Rai Ga Masu Yi Wa Ƙananan Yara Fyaɗe

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

Gwamnoni Sun Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Fashewar Tankar Mai A Neja

October 22, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.