• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahara Sun Kai Hari Ofishin ‘Yan Sanda A Kogi

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
Mahara Sun Kai Hari Ofishin ‘Yan Sanda A Kogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wane ba sun kai hari ofishin ‘yan sanda da ke Eika-Ohizenyi a karamar hukumar Okehi a Jihar Kogi, inda suka kashe wani jami’in dan sanda mai suna Mista Jibril, wanda aka fi sani da ‘Yellow’.

Wani mazaunin yankun mai suna Mallam Momoh Abubakar, ya tabbatar wa da wakilinmu cewar, ‘yan bindigar sun kai harin da misalin karfe 12:15 ma dare, inda suka jefa wani abu mai fashewa ofishin, lamarin da ya sanya daukacin al’ummar yankin tashi daga bacci.

  • Peter Obi Ya Jajantawa Ekweremadu Kan Cafke Shi Da Aka Yi a Burtaniya
  • Macizai Da Kunamu Na Barazana Ga Rayukan Mutanen Da Aka Sace A Harin Jirgin Kasa

Ya kara da cewa ‘yan bindigar sun dauki tsawon awa biyu suna sha’aninsu a yankin ba tare da an samu dauki daga jami’an tsaro ba.

Sannan ya ce jami’in dan sanda guda daya da ke aiki a lokacin ya rasa ransa, yayin da kuma suka cinna wa motar aikin ‘yan sandan wuta.

“Ina son amfani da wannan dama don jan hankalin jami’an tsaro da su zage damtse wajen dakile irin wannan hari da aka shafe awa biyu ba tare da kawo dauki ba.

Labarai Masu Nasaba

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 10 A Jihar Neja

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

“Harin farko da aka kai ofishin ‘yan sandan ranar Juma’a ne shekaru biyar da suka wuce, wannan ma kuma ranar Juma’a aka yi kuma abun mamaki babu wanda aka cafke da ke da alaka da harin.

“A yanzu dana ke magana da kai, akwai firgici da tashin hankali a zukatan mutane. Muna rokon gwamnati ta kawo dauki saboda wannan yanki ba zai iya jurar hare-haren da ake kawo ba, in ji Abubakar.

A halin da ake ciki an ajiye gawar dan sandan da aka kashe a babban asibitin Obandege.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mista Edward Ebuka, ya tabbatar da faruwar harin.

Sai dai ya ce wanda suka kai harin ba zasu tsira ba, domin rundunar ‘yan sandan jihar zata bankado inda suka shiga.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FarmakiHariKogiKwamishinan 'Yan SandaMaharaMazaunin YankiOfishin 'Yan SandaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Peter Obi Ya Jajantawa Ekweremadu Kan Cafke Shi Da Aka Yi a Burtaniya

Next Post

Kotun Daukaka Kara Ta Yi Watsi Da Karar Buhari Kan Sashe Na 84(12) Na Dokar Zabe

Related

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Labarai

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 10 A Jihar Neja

1 hour ago
DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci
Manyan Labarai

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

3 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

4 hours ago
Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu
Labarai

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

5 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

7 hours ago
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
Manyan Labarai

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

8 hours ago
Next Post
Kotun Daukaka Kara Ta Yi Watsi Da Karar Buhari Kan Sashe Na 84(12) Na Dokar Zabe

Kotun Daukaka Kara Ta Yi Watsi Da Karar Buhari Kan Sashe Na 84(12) Na Dokar Zabe

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 10 A Jihar Neja

September 11, 2025
DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

September 11, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

September 11, 2025
Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

September 11, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

September 11, 2025
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

September 11, 2025
Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

September 10, 2025
Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

September 10, 2025
Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

September 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.