• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahukuntan Lai Ching-te Sun Salwantar Da Muradun Kasa Wajen Neman ’Yancin Kai Bisa Dogaro Da ’Yan Katsalandan Na Ketare

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Mahukuntan Lai Ching-te Sun Salwantar Da Muradun Kasa Wajen Neman ’Yancin Kai Bisa Dogaro Da ’Yan Katsalandan Na Ketare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Laraba, 26 ga watan Maris, ofishin kula da harkokin Taiwan na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gudanar da taron manema labarai da aka saba yi yau da kullum. 

A lokacin taron, wani dan jarida ya yi tambaya game da wai “rahoto” na baya-bayan nan da Hukumar Kula da Harkokin Taiwan (MAC) ta gabatar, wanda ya yi ikirarin cewa, bayanan da babban yankin Sin ya fitar cewa, mashigin tekun Taiwan ba hanyar ruwa ba ce ta kasa da kasa, an yi ne da nufin “rikitar da jama’a da kuma nuna adawa da ‘yancin Amurka na kai-komo, inda dan jaridar ya ce shin, “me za ku ce?”.

  • Yadda Binciken Kayan Tarihi Ke Zakulo Asalin Magabata Da Wayewar Kansu A Kasar Sin
  • Rasha Da Ukraine Sun Amince Da Tsagaita Wuta A Tekun Black Sea

Mai magana da yawun babban yankin Sin, Chen Binhua ya bayyana cewa, kasar Sin daya ce kwallin kwal a duniya, kuma Taiwan wani bangare ne na kasar Sin. Don haka dukkan bangarori biyu na mashigin Taiwan mallakin kasar Sin ne, kana kasar tana da cikakken ‘yanci a kansu, da kuma cikakken ikon mallakar mashigin Taiwan.

Jami’in ya kara da cewa, dokokin ruwa na kasa da kasa ba su amince da wani abu da ake kira da “ruwa na kasa da kasa ba.” Kuma kasar Sin tana mutunta hakkin zirga-zirgar dukkan kasashe a tekun Taiwan bisa tsarin dokokin kasar Sin da na kasa da kasa, ciki har da yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya kan dokar teku ta UNCLOS. Sai dai kuma, tana adawa da haramtattun ayyukan ko wace kasa da ke neman kalubalantar ’yanci da ikon mallaka na kasar Sin, da tsaronta, bisa fakewa da sunan “‘yancin kai-komo.”

Haka nan ya ce, mahukuntan Lai Ching-te, a kokarin ‘wai’ neman ’yancin kai, ta hanyar dogaro da ’yan katsalandan na kasashen waje, sun manta da iyaye da kakanninsu, suna ta kururuwa a bainar kasashen waje, tare da salwantar da muradun kasa ba tare da jin kunya ba. Kazalika, sun kirkiri abin da ake kira “rahoto” domin a yi la’akari da karkatattun ikiraran Amurka, tare da hada kai da ’yan katsalandan na waje a takalar fadarsu, inda jami’in ya karkare da cewa, irin wadannan ayyuka ba komai ba ne illa raini kuma zance ne kawai na banza. (Abdulrazaq Yahuza Jere).

Labarai Masu Nasaba

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar

Next Post

Kwalara Ta Kashe Mutum 14, Ana Zargin 886 Sun Kamu A Nijeriya – NCDC

Related

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

15 hours ago
CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025
Daga Birnin Sin

CMG Ya Watsa Shirin Musamman Na Bikin Duanwu Na 2025

16 hours ago
Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed
Daga Birnin Sin

Ministocin Wajen Sin Da Kamaru Sun Gana Kan Alakar Kasashensu Da Batun Kafa IOMed

17 hours ago
Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje

18 hours ago
Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici
Daga Birnin Sin

Hukumar Shiga Tsakani Za Ta Samar Da Sabbin Damammakin Sulhunta Rikici

20 hours ago
Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa
Daga Birnin Sin

Tsohuwar Firaministar New Zealand: Ya Dace A Koyi Dabarun Sin Na Raya Kasa

22 hours ago
Next Post
Kwalara Ta Kashe Mutum 14, Ana Zargin 886 Sun Kamu A Nijeriya – NCDC

Kwalara Ta Kashe Mutum 14, Ana Zargin 886 Sun Kamu A Nijeriya – NCDC

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

June 1, 2025
Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

Alfanu Da Rashin Alfanun Tallata Shirin Aure Tun Kafin Lokacin Ya Zo

June 1, 2025
Yadda Za Ki Hada Funkasonki

Yadda Za Ki Hada Funkasonki

June 1, 2025
Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu

May 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.