• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mahukuntan Lai Ching-te Sun Salwantar Da Muradun Kasa Wajen Neman ’Yancin Kai Bisa Dogaro Da ’Yan Katsalandan Na Ketare

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Mahukuntan Lai Ching-te Sun Salwantar Da Muradun Kasa Wajen Neman ’Yancin Kai Bisa Dogaro Da ’Yan Katsalandan Na Ketare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Laraba, 26 ga watan Maris, ofishin kula da harkokin Taiwan na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gudanar da taron manema labarai da aka saba yi yau da kullum. 

A lokacin taron, wani dan jarida ya yi tambaya game da wai “rahoto” na baya-bayan nan da Hukumar Kula da Harkokin Taiwan (MAC) ta gabatar, wanda ya yi ikirarin cewa, bayanan da babban yankin Sin ya fitar cewa, mashigin tekun Taiwan ba hanyar ruwa ba ce ta kasa da kasa, an yi ne da nufin “rikitar da jama’a da kuma nuna adawa da ‘yancin Amurka na kai-komo, inda dan jaridar ya ce shin, “me za ku ce?”.

  • Yadda Binciken Kayan Tarihi Ke Zakulo Asalin Magabata Da Wayewar Kansu A Kasar Sin
  • Rasha Da Ukraine Sun Amince Da Tsagaita Wuta A Tekun Black Sea

Mai magana da yawun babban yankin Sin, Chen Binhua ya bayyana cewa, kasar Sin daya ce kwallin kwal a duniya, kuma Taiwan wani bangare ne na kasar Sin. Don haka dukkan bangarori biyu na mashigin Taiwan mallakin kasar Sin ne, kana kasar tana da cikakken ‘yanci a kansu, da kuma cikakken ikon mallakar mashigin Taiwan.

Jami’in ya kara da cewa, dokokin ruwa na kasa da kasa ba su amince da wani abu da ake kira da “ruwa na kasa da kasa ba.” Kuma kasar Sin tana mutunta hakkin zirga-zirgar dukkan kasashe a tekun Taiwan bisa tsarin dokokin kasar Sin da na kasa da kasa, ciki har da yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya kan dokar teku ta UNCLOS. Sai dai kuma, tana adawa da haramtattun ayyukan ko wace kasa da ke neman kalubalantar ’yanci da ikon mallaka na kasar Sin, da tsaronta, bisa fakewa da sunan “‘yancin kai-komo.”

Haka nan ya ce, mahukuntan Lai Ching-te, a kokarin ‘wai’ neman ’yancin kai, ta hanyar dogaro da ’yan katsalandan na kasashen waje, sun manta da iyaye da kakanninsu, suna ta kururuwa a bainar kasashen waje, tare da salwantar da muradun kasa ba tare da jin kunya ba. Kazalika, sun kirkiri abin da ake kira “rahoto” domin a yi la’akari da karkatattun ikiraran Amurka, tare da hada kai da ’yan katsalandan na waje a takalar fadarsu, inda jami’in ya karkare da cewa, irin wadannan ayyuka ba komai ba ne illa raini kuma zance ne kawai na banza. (Abdulrazaq Yahuza Jere).

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar

Next Post

Kwalara Ta Kashe Mutum 14, Ana Zargin 886 Sun Kamu A Nijeriya – NCDC

Related

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

9 hours ago
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

10 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

12 hours ago
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya
Daga Birnin Sin

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

13 hours ago
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
Daga Birnin Sin

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

14 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

15 hours ago
Next Post
Kwalara Ta Kashe Mutum 14, Ana Zargin 886 Sun Kamu A Nijeriya – NCDC

Kwalara Ta Kashe Mutum 14, Ana Zargin 886 Sun Kamu A Nijeriya – NCDC

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.