• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 weeks ago
in Ra'ayi Riga
0
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana kira Madagarscar kasar Vanilla, sakamakon ingancin tsirran Vanilla da ake samarwa a kasar, har ma yawan Vanilla da ake samarwa a kasar da ma fitarwa zuwa ketare ya kai na farko a duniya. Kasar Amurka kuma sakamakon yawan Askirim da ake sayarwa a kasar, ta kasance kasar da take kan gaba a yawan shigowa da Vanilla daga kasar Madagascar. Sai dai munanan matakan haraji da Amurka ta dauka a kan kasa da kasa, ya haifar da cikas ga Madagarscar wajen fitar da Vanilla, matakin da har ya daga farashin Askirim da ake sayarwa a kasar. Daidai kamar yadda wani jami’in diplomasiyya na kasar Madagarscar ya fada, harajin da Amurka ta sanya yana haifar da tasiri ga ‘yan kasuwa da al’umma na kasar Madagarscar, sai dai a sa’i daya, yana kuma tasiri ga masu sayayya na cikin gidan Amurka. 

“Munafunci dodo ya kan ci mai shi”. A hakika yadda gwamnatin kasar Amurka ta dauki matakan haraji ba bisa ka’ida ba yana haifar da munanan illoli ga kanta. Ta fannin abinci, bayan matsalar karancin kwai da aka fuskanta a kasar Amurka a farkon bana, a watan Yunin da ya gabata, farashin naman sa ya hau har zuwa wani matsayin da ba a taba ganin irinsa ba a tarihi, inda farashin nikakken naman sa ya karu da kusan kaso 12% kwatankwacin makamancin lokacin bara. Ban da haka, ‘yan kasuwar shigar da kayayyaki daga waje na kasar sun yi gargadin cewa, sakamakon matakan haraji da gwamnatin kasar ta dauka, farashin tumatir, da na sauran ‘ya’yan itatuwa da ganyaye ma ka iya karuwa da sauri. Hasali ma dai, matakan haraji na haifar da matsaloli ga tattalin arziki na kasar. Rahoton da kamfanin General Motor na kasar ta fitar game da harkokin kudinta cikin rubu’i na biyu na bana ya nuna cewa, matakan haraji na gwamnatin Amurka ta dauka ya haddasa hasarori kimanin dalar Amurka biliyan 1.1 ga kamfanin, kuma ribar da ya ci ma ya ragu da kaso 35.4%. Sai kuma alkaluman da ma’aikatar kasuwanci ta kasar Amurka ta samar a karshen Yuni ya shaida cewa, alkaluman tattalin arziki GDP na kasar cikin rubu’i na farko na bana ya ragu da kaso 0.5% kwatankwacin rubu’in karshe na bara. Har ila yau, kamfanin Fitch Ratings ya rage hasashen da ya yi game da makomar kaso 1/4 na sana’o’in kasar Amurka har ya bayyana ta a matsayin tabarbarewa, bisa dalilin rashin tabbas da ake kara fuskanta da kuma raguwar saurin bunkasar tattalin arzikin kasar.

  • Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso
  • Gwamnonin Nijeriya Sun Yi Ta’aziyyar Waɗanda Suka Rasu A Ambaliyar Ruwa A Adamawa

A akasin haka, wani rahoton da hukumar kididdiga ta kasar Sin ta bayar kwanan nan game da tattalin arzikin kasar Sin cikin farkon rabin shekarar bana, ya nuna cewa, alkaluman tattalin arzikin GDP ya karu da 5.3% a kasar Sin. Wannan ba karamar nasara ba, musamman a yayin da kariyar ciniki ke addabar duniya tare da haifar da cikas ga farfadowar tattalin arzki, wanda ya shaida ingancin tattalin arzikin kasar Sin, tare da sake tabbatar da al’ummar duniya cewa, bude kofa yana samar da ci gaba, yayin da rufe kofa kan haifar da koma baya. A hakika, tun bayan kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin, saurin bunkasar kasar ta fannonin tattalin arziki da zaman al’umma ya tabbata ne sakamakon yadda kasar ke bude kofarta ga ketare, da ma aiwatar da hadin gwiwar cin moriyar juna da kasa da kasa. A sa’i daya kuma, babbar kasuwar kasar Sin, da fasahohin zamani da cikakken tsarin masana’antu na kasar su ma sun samar da alfanu ga kasa da kasa. Duba da cewa, a cikin ‘yan shekarun baya, kasar ta samar da gudummawar da ta kai kimanin kaso 30% na bunkasuwar tattalin arzikin duniya baki daya, lamarin da ya sa ta zama babban ginshikin bunkasuwar tattalin arzikin duniya.

Ko da yake har yanzu Amurka tana kare aniyarta ta sanya harajin da bai dace ba kan kasa da kasa, amma ko kadan kasar Sin ba za ta tsayar da bude kofarta da hadin gwiwa da sauran kasashe ba. A satin da ya wuce, kasar ta samu babban ci gaba wajen gina tashar ciniki marar shinge ta Hainan, inda ta sanar da cewa, za a fara aiwatar da tsarin aikin kwastam mai zaman kansa a duk fadin tsibirin Hainan tun daga ranar 18 ga watan Disamban bana. Wato ya zuwa lokacin, za a fadada nau’o’in hajojin da ake cire musu harajin kwastan daga 1900 na yanzu har zuwa 6600, adadin da ya kai kimanin kaso 74% na gaba dayan hajoji.

Amurka tana daukar munanan matakan haraji ne don neman cimma burinta na “mai da Amurka a gaba da komai”, mataki mai son kai ne wanda ba kawai ya lalata moriyar sauran kasashe, har ma da ita kanta. Kasar Sin a nata bangare, tana dukufa a kan bude kofarta ga ketare, don kowa ya ci moriya.

Labarai Masu Nasaba

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Jama’a, shin mene ne ra’ayinku?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

Next Post

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Related

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman
Ra'ayi Riga

Tunawa Da Tarihi Tana Da Ma’anar Musamman

6 days ago
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Ra'ayi Riga

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

1 week ago
Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu
Ra'ayi Riga

Mu Tuna Da Jinin Da Aka Zubar Don Kiyaye Hasken Da Muke Da Shi Yanzu

2 weeks ago
Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

2 weeks ago
Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe
Ra'ayi Riga

Yaran Gaza Suna Da Hakkin Rungumar Gobe

3 weeks ago
Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”
Ra'ayi Riga

Amurka: “Afirka Ba Ta Cikin Jerin Fannoni Da Muka Ba Da Fifiko A Kai”

3 weeks ago
Next Post
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

August 22, 2025
Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

Dalilin Da Ya Sa Gwamnatin Jihar Kuros Ribas Ta Yi Hadaka Da Hukumar NPA

August 22, 2025
Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

Yaushe Shugaban Kasa Zai Ba ‘Yan Matan Yobe Nasu Kyaututtukan

August 22, 2025
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

August 22, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

August 22, 2025
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.