• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta 10: Zababbun Sanatocin APC Na Arewa Ta Tsakiya Sun Yi Fatali Da Zabin APC

by Abubakar Abba
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Majalisa Ta 10: Zababbun Sanatocin APC Na Arewa Ta Tsakiya Sun Yi Fatali Da Zabin APC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zababbun Sanatocin da suka fito daga Arewa ta Tsakiya a karkashin jam’iyyu daban-daban, sun nuna rashin amincewa da mukaman shiyya da jam’iyyar APC ta sanar.

APC a shirin da ta yi, ta sahale wa Sanata Godswill Akpabio da ya fito daga shiyyar Kudu Maso Kudu ya zama shugaban majalisar dattawa a majalisar ta 10, inda kuma Sanata Barau Jibrin, daga Arewa Maso Yamma zai zama mataimakinsa.

  • Manyan Jami’an Kasashen Sin Da Amurka Sun Tattauna Game Da Alakar Kasashen Biyu
  • Wakilin Kasar Sin Zai Kai Ziyara Turai Dangane Da Samar Da Mafita Ga Rikicin Ukraine

Haka zalika, a majalisar wakilai kuwa APC ta sahalewaTajudeen Abass daga Arewa Maso Yamma da ya zama shugaban majalisar wakilai, inda Benjamin Kalu daga Kudu Maso Gabas zai zama mataimakinsa.

Hakan ya tilasta wa zababbun Sanatocin da suka fito daga Arewa Maso Tsakiya rubuta wa shugaban APC na kasa Abdullahi Adamu wasika, inda suka sanar masa da kin lamunta da matsayin na APC ta kasa.

Sun bayyana cewa, a cikin wannan tsarin, ba a sanya Arewa ta Tsakiya a ciki ba duk da cewa zababben shugaban kasa da mataimakinsa, ba daga shiyyar suka fito ba.

Labarai Masu Nasaba

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

Wasikar mai taken: matsayar da yan majalisa suka cimma kan shugabancin majalisa ta 10 kan shugabancin shiyya.

Sanatoci 18 ne suka rattaba hannu kan wasikar wadanda suka hada da, Sanata Mohammed Sani Musa daga Neja ta Gabas, Sanata Ashiru Oyelola Yisa daga Kwara ta Kudu, Sanata Sadik Umar Suleiman daga Kwara ta Arewa, Sanata Mustapha Saliu daga Kwara ta Tsakiya da kuma Sanata Isah Jibrin daga Kogi ta Gabas.

Sauran su ne, Sanata Abba Moro daga Benuwe ta Kudu, Sanata Godiya Akwashiki daga Nasarawa ta Arewa, Sanata Ahmed Aliyu Wadada daga Nasarawa ta Yamma, Sanata Ireti Kingibe daga Birnin Tarayya, Sanata Sunday Karimi Stebe daga Kogi ta Yamma, Sanata Sadiku Abubakar daga Kogi ta Tsakiya da kuma Sanata Peter Ndalikali Jiya daga Neja ta Kudu.

Har ila yau, sun kuma hada da Sanata Napoleon Binkap Bali daga Filato ta Kudu, Sanata Mwadkion Simon Dabou daga Filato ta Arewa, Sanata Diket Plang daga Filato ta Tsakiya, Sanata Mohammed O. Onawo daga Nasarawa ta Kudu, Sanata Emmanuel M. Udende daga Benuwe ta Gabas da kuma Sanata Titus Tartenger Zam daga Benuwe ta Yamma.

Wasikar ta ce, mu Sanatocin da muka fito daga Arewa ta Tsakiya mun gudanar da ganawa a ranar 8 ga watan Mayu 2023, inda a ganawar ne, muka cimma wannan matsaya, cewar shiyyarmu ta jima tana tabbatar da ci gaban siyasa a kasar nan kuma za ta ci gaba da yin hakan tare da ci gaba da goya wa zababben shugaban kasa baya.

A cewar wasikar shiyyar ta kuma samawar wa APC kuri’u kashi 41 a zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabirairu, saboda haka, ita ma shiyyar lokaci ya yi da za a rama mata.

Bisa wadanan hujojin, muna kira ga APC ta kasa da ta gaggauta janye matsayar da ta cimma kan tsarin mukaman shugabancin majalisar ta 10.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCMajalisa Ta 10
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaɓen Gwamna: INEC Ta Fitar Da Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓuɓɓukan Cike Gurbi Na Jihohin Kogi, Bayelsa Da Imo

Next Post

Yadda Likita Ya Yi Lalata Da Wata Mai Jinya A Asibitinsa A Jihar Kwara

Related

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

12 hours ago
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

14 hours ago
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

16 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

18 hours ago
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara
Manyan Labarai

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

21 hours ago
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

1 day ago
Next Post
An Cafke Wasu Mutane 2 Da Ake Zargi Da Kashe ‘Yan Sanda 3 A Delta

Yadda Likita Ya Yi Lalata Da Wata Mai Jinya A Asibitinsa A Jihar Kwara

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

July 30, 2025
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.