• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Za Ta Yi Bincike Kan Hakar Ma’adanai Da Kalubalen Tsaro A Arewa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Majalisa

A ranar Talata ne majalisar wakilai ta kuduri aniyar gudanar da cikakken bincike kan musabbabin ta’addanci da rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma, musamman yadda ake hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

An cimma matsayar ne biyo bayan amincewa da kudirin da Hon. Kabiru Mai-Palace, wanda ya nuna matukar damuwarsa kan yadda ake ci gaba da samun tabarbarewar rashin tsaro a yankin Arewa maso yammacin Nijeriya.

  • Manoman Kenya Na Kara Rungumar Fasahohin Inganta Noma Na Sin
  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Kama Kwale-kwale Da Muggan Kwayoyin Miliyan N200 A Legas

A muhawarar da ya jagoranta, Hon. Kabiru ya yi tir da karuwar tashe-tashen hankula da ‘yan bindiga ke yi a yankin Arewa maso gabashin Nijeriya, inda ya kai ga sace dalibai mata na jami’ar tarayya da ke Jihar Zamfara da kuma yin garkuwa da wasu masu yi wa kasa hidima (NYSC) lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa Jihar Sakkwato.

Ya kuma ambaci wasu abubuwan da suka faru na cin zarafin ‘yan Nijeriya da ba su ji ba ba su gani ba a jihohi daban-daban na yankin.

Bisa damuwa da wadannan abubuwan, Hon. Kabiru ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta tabbatar an sako duk wadanda aka sace tare da kama masu garkuwan domin hukunta su.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Ya kuma bukaci gwamnati da ta tura karin jami’an tsaro a wuraren da ake fama da tashin hankali a yankin.

A nasa martanin, Hon. Ismail Haruna ya bayar da shawarar yin gyaran fuska na sanya sassan yankin Arewa maso gabas, musamman Jihar Bauchi cikin addu’o’i.

A bangarensa, Hon. Suleiman Gummi ya jaddada bukatar hadin kai tsakanin jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki a yaki da ‘yan fashi da makami a yankin Arewa maso yamma.

Ya yi kira ga majalisar da ta bai wa mashawarcin shugaban kasa kan sha’annin tsaro shawara kan shirya taro na musamman domin tabbatar da cewa duk masu ruwa da tsaki sun hada kai wajen magance matsalar ‘yan bindiga da kuma rashin tsaro a yankin.

Shi ma da yake jawabi, Hon. Abdullahi Balarabe ya jaddada bukatar tabbatar da shigar da ‘yan kasar cikin tsare-tsaren magance matsalolin ‘yan bindiga da kuma na rashin tsaro da suka addabi yankin Arewa.

A nasa gudunmawar, Hon. Isa Mohammed ya bukaci gwamnatin tarayya da ta tabbatar da aiwatar da kudurorin da aka cimma da gwamnatin da ta gabata.

A ci gaba da kokarin da ake yi na samar da dawwamammen maslaha kan kalubalen tsaro da ake fuskanta, ya bukaci a gudanar da bincike kan ayyukan masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a yankin, wanda a cewarsa shi ne ke haifar da karuwar rashin tsaro a Arewa.

Yayin da yake bayyana ra’ayinsa, Hon. Bello Kaoje ya jaddada wajabcin gudanar da cikakken bincike kan musabbabin ta’adda da rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma, musamman nazarin alakarsu da hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

Don haka, majalisar ta umarci kwamitocin hadin gwiwa kan harkokin tsaro da su tabbatar da daukar mataki na gaba.

A yayin zaman, mataimakin shugaban majalisar wakilai, Hon. Benjamin Kalu ya bayar da umarnin rufe dukkanin kwamitocin wucin gadi na majalisar domin samar da dama ga kwamitoci na dindindin don gudanar da ayyukansu na doka.

An umurci shugabannin kwamitocin wucin gadi da su gabatar da rahotonsu, sannan kwamitocin majalisa su ci gaba daga inda suka tsaya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama
Manyan Labarai

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Next Post
Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana

Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.