• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Za Ta Yi Bincike Kan Hakar Ma’adanai Da Kalubalen Tsaro A Arewa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Majalisa Za Ta Yi Bincike Kan Hakar Ma’adanai Da Kalubalen Tsaro A Arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talata ne majalisar wakilai ta kuduri aniyar gudanar da cikakken bincike kan musabbabin ta’addanci da rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma, musamman yadda ake hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

An cimma matsayar ne biyo bayan amincewa da kudirin da Hon. Kabiru Mai-Palace, wanda ya nuna matukar damuwarsa kan yadda ake ci gaba da samun tabarbarewar rashin tsaro a yankin Arewa maso yammacin Nijeriya.

  • Manoman Kenya Na Kara Rungumar Fasahohin Inganta Noma Na Sin
  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Kama Kwale-kwale Da Muggan Kwayoyin Miliyan N200 A Legas

A muhawarar da ya jagoranta, Hon. Kabiru ya yi tir da karuwar tashe-tashen hankula da ‘yan bindiga ke yi a yankin Arewa maso gabashin Nijeriya, inda ya kai ga sace dalibai mata na jami’ar tarayya da ke Jihar Zamfara da kuma yin garkuwa da wasu masu yi wa kasa hidima (NYSC) lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa Jihar Sakkwato.

Ya kuma ambaci wasu abubuwan da suka faru na cin zarafin ‘yan Nijeriya da ba su ji ba ba su gani ba a jihohi daban-daban na yankin.

Bisa damuwa da wadannan abubuwan, Hon. Kabiru ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta tabbatar an sako duk wadanda aka sace tare da kama masu garkuwan domin hukunta su.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

Ya kuma bukaci gwamnati da ta tura karin jami’an tsaro a wuraren da ake fama da tashin hankali a yankin.

A nasa martanin, Hon. Ismail Haruna ya bayar da shawarar yin gyaran fuska na sanya sassan yankin Arewa maso gabas, musamman Jihar Bauchi cikin addu’o’i.

A bangarensa, Hon. Suleiman Gummi ya jaddada bukatar hadin kai tsakanin jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki a yaki da ‘yan fashi da makami a yankin Arewa maso yamma.

Ya yi kira ga majalisar da ta bai wa mashawarcin shugaban kasa kan sha’annin tsaro shawara kan shirya taro na musamman domin tabbatar da cewa duk masu ruwa da tsaki sun hada kai wajen magance matsalar ‘yan bindiga da kuma rashin tsaro a yankin.

Shi ma da yake jawabi, Hon. Abdullahi Balarabe ya jaddada bukatar tabbatar da shigar da ‘yan kasar cikin tsare-tsaren magance matsalolin ‘yan bindiga da kuma na rashin tsaro da suka addabi yankin Arewa.

A nasa gudunmawar, Hon. Isa Mohammed ya bukaci gwamnatin tarayya da ta tabbatar da aiwatar da kudurorin da aka cimma da gwamnatin da ta gabata.

A ci gaba da kokarin da ake yi na samar da dawwamammen maslaha kan kalubalen tsaro da ake fuskanta, ya bukaci a gudanar da bincike kan ayyukan masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a yankin, wanda a cewarsa shi ne ke haifar da karuwar rashin tsaro a Arewa.

Yayin da yake bayyana ra’ayinsa, Hon. Bello Kaoje ya jaddada wajabcin gudanar da cikakken bincike kan musabbabin ta’adda da rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma, musamman nazarin alakarsu da hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

Don haka, majalisar ta umarci kwamitocin hadin gwiwa kan harkokin tsaro da su tabbatar da daukar mataki na gaba.

A yayin zaman, mataimakin shugaban majalisar wakilai, Hon. Benjamin Kalu ya bayar da umarnin rufe dukkanin kwamitocin wucin gadi na majalisar domin samar da dama ga kwamitoci na dindindin don gudanar da ayyukansu na doka.

An umurci shugabannin kwamitocin wucin gadi da su gabatar da rahotonsu, sannan kwamitocin majalisa su ci gaba daga inda suka tsaya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsantseni Da Gudun Duniya Na Annabi S.A.W (2)

Next Post

Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana

Related

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

3 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

5 hours ago
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja
Manyan Labarai

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

7 hours ago
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno
Manyan Labarai

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

9 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

1 day ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

2 days ago
Next Post
Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana

Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana

LABARAI MASU NASABA

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Gwamnatin Sakkwato Ta Ƙaddamar Da Sababbin Motoci 30, Don Bunƙasa Sha’anin Sufuri A Jihar

Super Falcons Sun Iso Abuja Ɗauke Da Kofin WAFCON

July 28, 2025
Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

July 28, 2025
Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500

Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500

July 28, 2025
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

July 28, 2025
Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

Sojoji, DSS Sun Hallaka Ƴan Bindiga 45 A Neja

July 28, 2025
SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.