ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Za Ta Yi Bincike Kan Hakar Ma’adanai Da Kalubalen Tsaro A Arewa

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Majalisa

A ranar Talata ne majalisar wakilai ta kuduri aniyar gudanar da cikakken bincike kan musabbabin ta’addanci da rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma, musamman yadda ake hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

An cimma matsayar ne biyo bayan amincewa da kudirin da Hon. Kabiru Mai-Palace, wanda ya nuna matukar damuwarsa kan yadda ake ci gaba da samun tabarbarewar rashin tsaro a yankin Arewa maso yammacin Nijeriya.

  • Manoman Kenya Na Kara Rungumar Fasahohin Inganta Noma Na Sin
  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Kama Kwale-kwale Da Muggan Kwayoyin Miliyan N200 A Legas

A muhawarar da ya jagoranta, Hon. Kabiru ya yi tir da karuwar tashe-tashen hankula da ‘yan bindiga ke yi a yankin Arewa maso gabashin Nijeriya, inda ya kai ga sace dalibai mata na jami’ar tarayya da ke Jihar Zamfara da kuma yin garkuwa da wasu masu yi wa kasa hidima (NYSC) lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa Jihar Sakkwato.

ADVERTISEMENT

Ya kuma ambaci wasu abubuwan da suka faru na cin zarafin ‘yan Nijeriya da ba su ji ba ba su gani ba a jihohi daban-daban na yankin.

Bisa damuwa da wadannan abubuwan, Hon. Kabiru ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta tabbatar an sako duk wadanda aka sace tare da kama masu garkuwan domin hukunta su.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Ya kuma bukaci gwamnati da ta tura karin jami’an tsaro a wuraren da ake fama da tashin hankali a yankin.

A nasa martanin, Hon. Ismail Haruna ya bayar da shawarar yin gyaran fuska na sanya sassan yankin Arewa maso gabas, musamman Jihar Bauchi cikin addu’o’i.

A bangarensa, Hon. Suleiman Gummi ya jaddada bukatar hadin kai tsakanin jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki a yaki da ‘yan fashi da makami a yankin Arewa maso yamma.

Ya yi kira ga majalisar da ta bai wa mashawarcin shugaban kasa kan sha’annin tsaro shawara kan shirya taro na musamman domin tabbatar da cewa duk masu ruwa da tsaki sun hada kai wajen magance matsalar ‘yan bindiga da kuma rashin tsaro a yankin.

Shi ma da yake jawabi, Hon. Abdullahi Balarabe ya jaddada bukatar tabbatar da shigar da ‘yan kasar cikin tsare-tsaren magance matsalolin ‘yan bindiga da kuma na rashin tsaro da suka addabi yankin Arewa.

A nasa gudunmawar, Hon. Isa Mohammed ya bukaci gwamnatin tarayya da ta tabbatar da aiwatar da kudurorin da aka cimma da gwamnatin da ta gabata.

A ci gaba da kokarin da ake yi na samar da dawwamammen maslaha kan kalubalen tsaro da ake fuskanta, ya bukaci a gudanar da bincike kan ayyukan masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a yankin, wanda a cewarsa shi ne ke haifar da karuwar rashin tsaro a Arewa.

Yayin da yake bayyana ra’ayinsa, Hon. Bello Kaoje ya jaddada wajabcin gudanar da cikakken bincike kan musabbabin ta’adda da rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma, musamman nazarin alakarsu da hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

Don haka, majalisar ta umarci kwamitocin hadin gwiwa kan harkokin tsaro da su tabbatar da daukar mataki na gaba.

A yayin zaman, mataimakin shugaban majalisar wakilai, Hon. Benjamin Kalu ya bayar da umarnin rufe dukkanin kwamitocin wucin gadi na majalisar domin samar da dama ga kwamitoci na dindindin don gudanar da ayyukansu na doka.

An umurci shugabannin kwamitocin wucin gadi da su gabatar da rahotonsu, sannan kwamitocin majalisa su ci gaba daga inda suka tsaya.

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana

Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.