ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Za Ta Yi Bincike Kan Hakar Ma’adanai Da Kalubalen Tsaro A Arewa

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Majalisa

A ranar Talata ne majalisar wakilai ta kuduri aniyar gudanar da cikakken bincike kan musabbabin ta’addanci da rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma, musamman yadda ake hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

An cimma matsayar ne biyo bayan amincewa da kudirin da Hon. Kabiru Mai-Palace, wanda ya nuna matukar damuwarsa kan yadda ake ci gaba da samun tabarbarewar rashin tsaro a yankin Arewa maso yammacin Nijeriya.

  • Manoman Kenya Na Kara Rungumar Fasahohin Inganta Noma Na Sin
  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Kama Kwale-kwale Da Muggan Kwayoyin Miliyan N200 A Legas

A muhawarar da ya jagoranta, Hon. Kabiru ya yi tir da karuwar tashe-tashen hankula da ‘yan bindiga ke yi a yankin Arewa maso gabashin Nijeriya, inda ya kai ga sace dalibai mata na jami’ar tarayya da ke Jihar Zamfara da kuma yin garkuwa da wasu masu yi wa kasa hidima (NYSC) lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa Jihar Sakkwato.

ADVERTISEMENT

Ya kuma ambaci wasu abubuwan da suka faru na cin zarafin ‘yan Nijeriya da ba su ji ba ba su gani ba a jihohi daban-daban na yankin.

Bisa damuwa da wadannan abubuwan, Hon. Kabiru ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta tabbatar an sako duk wadanda aka sace tare da kama masu garkuwan domin hukunta su.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Ya kuma bukaci gwamnati da ta tura karin jami’an tsaro a wuraren da ake fama da tashin hankali a yankin.

A nasa martanin, Hon. Ismail Haruna ya bayar da shawarar yin gyaran fuska na sanya sassan yankin Arewa maso gabas, musamman Jihar Bauchi cikin addu’o’i.

A bangarensa, Hon. Suleiman Gummi ya jaddada bukatar hadin kai tsakanin jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki a yaki da ‘yan fashi da makami a yankin Arewa maso yamma.

Ya yi kira ga majalisar da ta bai wa mashawarcin shugaban kasa kan sha’annin tsaro shawara kan shirya taro na musamman domin tabbatar da cewa duk masu ruwa da tsaki sun hada kai wajen magance matsalar ‘yan bindiga da kuma rashin tsaro a yankin.

Shi ma da yake jawabi, Hon. Abdullahi Balarabe ya jaddada bukatar tabbatar da shigar da ‘yan kasar cikin tsare-tsaren magance matsalolin ‘yan bindiga da kuma na rashin tsaro da suka addabi yankin Arewa.

A nasa gudunmawar, Hon. Isa Mohammed ya bukaci gwamnatin tarayya da ta tabbatar da aiwatar da kudurorin da aka cimma da gwamnatin da ta gabata.

A ci gaba da kokarin da ake yi na samar da dawwamammen maslaha kan kalubalen tsaro da ake fuskanta, ya bukaci a gudanar da bincike kan ayyukan masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a yankin, wanda a cewarsa shi ne ke haifar da karuwar rashin tsaro a Arewa.

Yayin da yake bayyana ra’ayinsa, Hon. Bello Kaoje ya jaddada wajabcin gudanar da cikakken bincike kan musabbabin ta’adda da rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma, musamman nazarin alakarsu da hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

Don haka, majalisar ta umarci kwamitocin hadin gwiwa kan harkokin tsaro da su tabbatar da daukar mataki na gaba.

A yayin zaman, mataimakin shugaban majalisar wakilai, Hon. Benjamin Kalu ya bayar da umarnin rufe dukkanin kwamitocin wucin gadi na majalisar domin samar da dama ga kwamitoci na dindindin don gudanar da ayyukansu na doka.

An umurci shugabannin kwamitocin wucin gadi da su gabatar da rahotonsu, sannan kwamitocin majalisa su ci gaba daga inda suka tsaya.

Majalisa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana

Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.