• English
  • Business News
Sunday, September 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Kafa Kwamitin Sa Ido Kan Gwamnatin Riƙo A Ribas

by Sadiq
5 months ago
in Labarai
0
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawa ta kafa wani kwamiti mai mutum 18 domin sa ido da bin diddigin yadda gwamnan riƙo na Jihar Ribas, Vice Admiral Ibok Ete Ibas (mai ritaya), ke gudanar da mulki tun bayan ayyanar dokar ta-ɓaci a jihar.

Shugaban. Majalisar, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana hakan yayin zaman majalisar na ranar Talata, inda ya ce kafa kwamitin zai taimaka wajen tabbatar da shugabanci na gaskiya da kuma ganin an bi doka yadda ya kamata a jihar.

  • EFCC Ta Kama Matashi A Kaduna Bisa Zargin Wulaƙanta Naira A Bidiyon Barkwanci
  • Za A Gudanar Da Taron Tallata Fim Din “Red Silk” A Moscow

Ya ce, “Wannan mataki wani ɓangare ne na ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya da bin doka a Jihar Ribas, ba tare da wata ɓoyayyar manufa ba.”

Kwamitin, wanda shugaban masu rinjaye, Sanata Opeyemi Bamidele ke jagoranta, ya ƙunshi Sanata Adamu Aliero, Osita Izunaso, Osita Ngwu, Kaka Shehu, Aminu Abass, Tokunbo Abiru, da Adeniyi Adebire, tare da wasu ƙarin mambobi.

Tun a watan Maris ne shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas saboda rikicin siyasa da ya ɓarke tsakanin gwamnan jihar, Siminalayi Fubara na jam’iyyar PDP, da tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike, wanda yanzu ke cikin gwamnati a matakin tarayya a matsayin minista.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja

SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook

Rikicin ya janyo zaman ɗari-ɗari a jihar, lamarin da ya sa shugaban ƙasa ya tsoma baki domin kare zaman lafiya da doka a jihar.

Gwamnan riƙo Ibok Ete Ibas ne aka ɗora don tafiyar da mulki har sai an samu daidaito a siyasar jihar.

Ana sa ran kwamitin za ta kai rahoto a duk matakin da take gani ya kamata a ɗauka domin kare mulkin dimokuraɗiyya da kwanciyar hankali a Jihar Ribas, wadda ke daga cikin muhimman jahohin da ke da tasiri a tattalin arziƙin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KwamitiMajalisar DattawaMulkiRibasRikiciSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Ilimi Ya Ce Hana Satar Amsa Ne Ya Sa Ɗalibai Suka Faɗi JAMB A Bana

Next Post

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

Related

Ribas
Labarai

Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja

33 minutes ago
SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook
Manyan Labarai

SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook

2 hours ago
Komai Nisan Dare Gari Zai Waye
Ra'ayi Riga

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

2 hours ago
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 

5 hours ago
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku
Labarai

2027: ‘Ku Yi Zaɓe Bisa Ga Ra’ayin Kanku, Ba Lura Da Ƙabila Ko Yanki Ba’, – Atiku Ga ‘Yan Nijeriya

5 hours ago
Ribas
Labarai

An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina

6 hours ago
Next Post
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Son Karfafa Hadin Gwiwar Masana’antu Da Dukkan Bangarori

Kasar Sin Na Son Karfafa Hadin Gwiwar Masana’antu Da Dukkan Bangarori

September 21, 2025
Ribas

Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja

September 21, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Bayyana Ra’ayin Kasar Kan Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Bayyana Ra’ayin Kasar Kan Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

September 21, 2025
SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook

SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook

September 21, 2025
Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

September 21, 2025
Ribas

Babu Wanda Ya Jawo Ra’ayina  Zuwa Masana’antar Kannywood —Umar Hassan (2)

September 21, 2025
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Manchester City 

September 21, 2025
Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

September 21, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

2027: ‘Ku Yi Zaɓe Bisa Ga Ra’ayin Kanku, Ba Lura Da Ƙabila Ko Yanki Ba’, – Atiku Ga ‘Yan Nijeriya

September 21, 2025
Ribas

An Cafke Wani Magidanci Da Lafin Sojan Gona A Katsina

September 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.