• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Ta Kafa Kwamitin Sa Ido Kan Gwamnatin Riƙo A Ribas

by Sadiq
3 months ago
in Labarai
0
Majalisa Ta Goyi Bayan CBN Kan Sauya Fasalin Naira Bayan Tafka Muhawara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Dattawa ta kafa wani kwamiti mai mutum 18 domin sa ido da bin diddigin yadda gwamnan riƙo na Jihar Ribas, Vice Admiral Ibok Ete Ibas (mai ritaya), ke gudanar da mulki tun bayan ayyanar dokar ta-ɓaci a jihar.

Shugaban. Majalisar, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana hakan yayin zaman majalisar na ranar Talata, inda ya ce kafa kwamitin zai taimaka wajen tabbatar da shugabanci na gaskiya da kuma ganin an bi doka yadda ya kamata a jihar.

  • EFCC Ta Kama Matashi A Kaduna Bisa Zargin Wulaƙanta Naira A Bidiyon Barkwanci
  • Za A Gudanar Da Taron Tallata Fim Din “Red Silk” A Moscow

Ya ce, “Wannan mataki wani ɓangare ne na ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya da bin doka a Jihar Ribas, ba tare da wata ɓoyayyar manufa ba.”

Kwamitin, wanda shugaban masu rinjaye, Sanata Opeyemi Bamidele ke jagoranta, ya ƙunshi Sanata Adamu Aliero, Osita Izunaso, Osita Ngwu, Kaka Shehu, Aminu Abass, Tokunbo Abiru, da Adeniyi Adebire, tare da wasu ƙarin mambobi.

Tun a watan Maris ne shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas saboda rikicin siyasa da ya ɓarke tsakanin gwamnan jihar, Siminalayi Fubara na jam’iyyar PDP, da tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike, wanda yanzu ke cikin gwamnati a matakin tarayya a matsayin minista.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

Rikicin ya janyo zaman ɗari-ɗari a jihar, lamarin da ya sa shugaban ƙasa ya tsoma baki domin kare zaman lafiya da doka a jihar.

Gwamnan riƙo Ibok Ete Ibas ne aka ɗora don tafiyar da mulki har sai an samu daidaito a siyasar jihar.

Ana sa ran kwamitin za ta kai rahoto a duk matakin da take gani ya kamata a ɗauka domin kare mulkin dimokuraɗiyya da kwanciyar hankali a Jihar Ribas, wadda ke daga cikin muhimman jahohin da ke da tasiri a tattalin arziƙin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KwamitiMajalisar DattawaMulkiRibasRikiciSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ministan Ilimi Ya Ce Hana Satar Amsa Ne Ya Sa Ɗalibai Suka Faɗi JAMB A Bana

Next Post

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

Related

Borno
Labarai

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

22 minutes ago
Yajin aiki
Labarai

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

1 hour ago
Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19
Labarai

Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

4 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

15 hours ago
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam
Labarai

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

16 hours ago
Next Post
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

LABARAI MASU NASABA

Borno

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

August 11, 2025
Yajin aiki

Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba

August 11, 2025
Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19

August 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

August 11, 2025
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK

August 11, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.