• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dattawa Zata Tantance Sunayen Ministocin Buhari Ranar Laraba Mai Zuwa

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Majalisar Dattawa Zata Tantance Sunayen Ministocin Buhari Ranar Laraba Mai Zuwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan, ya ce a mako mai zuwa ne majalisar za ta tantance sunayen ministoci bakwai da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika wa zauren majalisar domin tantance su.

Lawan ya bayyana hakan ne a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, gabanin dage zaman majalisar.

  • Buhari Ya Bukaci ‘Yan Majalisa Da Su Tabbatar Da Sabbin Sunayen Ministoci Da Ya Aike
  • An Fafata Da Lawan A Zaben Fidda Gwanin Sanatocin Yobe – Shugaban APC

“Za a tantance wadanda aka nada a matsayin ministoci ranar Laraba, mako mai zuwa”, in ji Lawan.

Shugaba Buhari, a wata wasika mai dauke da kwanan watan 15 ga watan Yuni, 2022, ya bukaci majalisar dattijai ta tabbatar da tantance sunayen ministoci bakwai.

Ya ce an gabatar da bukatar tabbatar da sashe na 147(2) na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya na shekarar 1999 kamar yadda aka gyara.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Wadanda aka nada domin tantancewa sun hada da: Henry Ikechukwu Ikoh – Jihar Abia; Umana Okon Umana – Jihar Akwa Ibom; Ekumankama Joseph Nkama- Jihar Ebonyi; da Goodluck Nanah Opiah – Jihar Imo.

Sauran sun hada da Umar Ibrahim El-Yakub – Jihar Kano; Ademola Adewole Adegoroye – Jihar Ondo; da Odum Udi – Jihar Ribas.

Hakazalika, Majalisar Dattawa a jiya ta tabbatar da nadin Dr. Hale Gabriel Longpet (Plateau) a matsayin Kwamishinan Zabe na Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC).

Tabbatar da Longpet ya biyo bayan la’akari da rahoton kwamitin da ke kan al’amuran zabe.

Shugaban kwamitin, Sanata Kabiru Gaya (Kano ta Kudu), a jawabinsa, ya ce an gabatar da nadin Longpet ne bisa tanadin sashe na 154 (1) na kundin tsarin mulkin Tarayyar Najeriya, 1999 (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima).

Ya bayyana cewa wanda aka zaba a lokacin da ya gurfana gaban kwamitin domin tantancewa, ya bayar da bayani dangane da rayuwarsa, kwarewar aikinsa, dacewarsa, cancantarsa ​​da amincinsa na nadinsa a matsayin kwamishinan hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Ya ce mambobin Kwamitin sun yaba da kyakkyawan tsarin Karatu da kuma gamsassun amsoshi ga tambayoyin da aka gabatar.

Bayan haka, an tabbatar da wanda aka zaba a

zauren.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuharimajalisaMinistociSanatoci
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Mutane 3, Da Sace Wata Mata A Katsina

Next Post

Majalisar Malaman Musulunci Ta Oyo Sun Nada Ganduje Sarautar ALAUDDEN Na Yarbawa

Related

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

46 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

10 hours ago
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

11 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

13 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

15 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da É—umi-É—uminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

17 hours ago
Next Post
Majalisar Malaman Musulunci Ta Oyo Sun Nada Ganduje Sarautar ALAUDDEN Na Yarbawa

Majalisar Malaman Musulunci Ta Oyo Sun Nada Ganduje Sarautar ALAUDDEN Na Yarbawa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin HaÆ™ar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.