• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dinkin Duniya Ta Koka Kan Rashin Tallafa Wa Mata Manoma A Nijeriya

by Sulaiman and Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Ambaliyar Ruwa A Jihar Bayelsa Kalubale Ne Mai Girman Gaske – Majalisar Dinkin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin wakiliyar mata a Majalisar dinkin duniya, Lansana Wonneh ya koka kan yadda mata manoma da ke a karkara a kasar nan, ba samun tallafin a kan Sana’ar ta su ta yin noma.

Ya sanar da cewa, matan manoma a karkara, na bayar da gagarumar gudunmawa,musamman wajen kara bunkasa samar da abinci da kuma kara habaka tattalin arzikin kasar nan.

  • Ambaliyar Ruwa: Manoma Sun Samu Tallafin Asusun Bunkasa Noma

Ya sanar da hakan ne a wani taro a garin Kalaba a kan bikin zagayowar ranar mata manoma da ke a karkara ta duniya, inda ya ci gaba da cewa, an shirya taron ne domin a kara wa matan manoma karkashin kokarin da suke yi na samar da wadataccen abinci, musamman mai gina jiki a daukacin fadin Nijeriya.

Wonneh ya ce an shirya taron ne domin zaburar da mata mazauna karkarar da ke kokarin samarwa, da sarrafawa, hadi da tattata abinci don ciyar da al’umma, duk da watsi da su da ake yi a kasar.
Ya ce Majalisar Dinkin Duniya za ta hada kai da Gwamnatin Nijeriya domin kawo gyara a lamarin.

“An shirya taron ne domin a kara wa matan manoma karkashin kokarin da suke yi na samar da wadataccen abinci, musamman mai gina jiki a daukacin fadin Nijeriya da kumakara karfafa masu gwiwa don su kara samar wa da kawunan su da kudaden shiga don sana’ar ta su ta kara bunkasa”.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

A cewar Wonneh ya zama wajibi matan manoman da ke a karkara a dinga tallafa mUsu, musamman idan aka yi dubi da irin wahalhalun da suke fuskanta a lokacin gudanar da aikin na su na noman.

Ya sanar da cewa, burin da majalisar ta ke da shi a kan matan manoman na karkara shine, aga suna samun kayan aikin noman, musamman na zamani da kuma samar masu da wadatattun kudade.

Ya yi nuni da cewa, tallafin zai taimaka masu matuka wajen kara mayar da hankali a kan gudanar da aikin na su na noman.
A wata sabuwa kuwa, an ankarar da gwamatin tarayya kan mahimmancin da ke tattare da san ya mata manoma a daukacin fadin kasar nan a cikin shirye-shiyen aikin noma na kasar.

Wannan ankararwar ta fito ne daga bakin Hajiya Amina Jibrin ita ce, shugabar kungiyar mata manoma kanana da da ke a kasar nan.
A Jawabin da ta yi a kwanan baya a bikin ranar abinci ta duniya Hajiya Amina Jibrin ta bukaci da a tallafa wa manoman, musamman idana aka yi dubi da yadda iftila’in ambaliyar ruwan sama ta yiwa wasu manoman kasar nan barna a gonakansu, inda ta sanar da cewa, matan manoma musamman na bukatar tallafi domin su samu samar ci gaba da yin noman da kuma tsyawa da kafafunsu.

Shugabar ta ci gaba da cewa, ya zama wajibi mahukunta a kasar nan da su samar da dokokin da za su bayar da damar tallafa wa kananan manoma, musamman a dora su a kan yin inshorar aikin noma.

Hajiya Amina ta kuma shawarci gwamnatin jihar Bauchi ta kebe kanana manoman da ke a fadin jihar, bisa yarjejeniyar da aka sa wa hannu ta Maputo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Ware Naira Miliyan 300 A Matsayin Kudin Karatun Daliban Kano Da Ke Karatu A Waje

Next Post

Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro

Related

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

6 days ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

6 days ago
Sin Ta Gina Cibiyoyin Fasahar Aikin Gona Na Gwaji Guda 24 A Afirka
Noma Da Kiwo

Muhimman Dalilan Kirkiro Da Shirin Inganta Aikin Noma ‘SAPZ’

2 weeks ago
Dalilin Nijeriya Na Kulla Yarjejeniya Da Kasar Sin Kan Noman Rake
Noma Da Kiwo

Dalilin Nijeriya Na Kulla Yarjejeniya Da Kasar Sin Kan Noman Rake

2 weeks ago
Nazari Kan Amfanin Noman Kanumfari
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Amfanin Noman Kanumfari

2 weeks ago
Cutar Da Ke Kassara Gonakin Tumatir Ta Sake Bulla A Jihar Kano
Noma Da Kiwo

Cutar Da Ke Kassara Gonakin Tumatir Ta Sake Bulla A Jihar Kano

3 weeks ago
Next Post
Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro

Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.