• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dinkin Duniya Ta Koka Kan Rashin Tallafa Wa Mata Manoma A Nijeriya

by Sulaiman and Abubakar Abba
3 years ago
Duniya

Mataimakin wakiliyar mata a Majalisar dinkin duniya, Lansana Wonneh ya koka kan yadda mata manoma da ke a karkara a kasar nan, ba samun tallafin a kan Sana’ar ta su ta yin noma.

Ya sanar da cewa, matan manoma a karkara, na bayar da gagarumar gudunmawa,musamman wajen kara bunkasa samar da abinci da kuma kara habaka tattalin arzikin kasar nan.

  • Ambaliyar Ruwa: Manoma Sun Samu Tallafin Asusun Bunkasa Noma

Ya sanar da hakan ne a wani taro a garin Kalaba a kan bikin zagayowar ranar mata manoma da ke a karkara ta duniya, inda ya ci gaba da cewa, an shirya taron ne domin a kara wa matan manoma karkashin kokarin da suke yi na samar da wadataccen abinci, musamman mai gina jiki a daukacin fadin Nijeriya.

Wonneh ya ce an shirya taron ne domin zaburar da mata mazauna karkarar da ke kokarin samarwa, da sarrafawa, hadi da tattata abinci don ciyar da al’umma, duk da watsi da su da ake yi a kasar.
Ya ce Majalisar Dinkin Duniya za ta hada kai da Gwamnatin Nijeriya domin kawo gyara a lamarin.

“An shirya taron ne domin a kara wa matan manoma karkashin kokarin da suke yi na samar da wadataccen abinci, musamman mai gina jiki a daukacin fadin Nijeriya da kumakara karfafa masu gwiwa don su kara samar wa da kawunan su da kudaden shiga don sana’ar ta su ta kara bunkasa”.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

A cewar Wonneh ya zama wajibi matan manoman da ke a karkara a dinga tallafa mUsu, musamman idan aka yi dubi da irin wahalhalun da suke fuskanta a lokacin gudanar da aikin na su na noman.

Ya sanar da cewa, burin da majalisar ta ke da shi a kan matan manoman na karkara shine, aga suna samun kayan aikin noman, musamman na zamani da kuma samar masu da wadatattun kudade.

Ya yi nuni da cewa, tallafin zai taimaka masu matuka wajen kara mayar da hankali a kan gudanar da aikin na su na noman.
A wata sabuwa kuwa, an ankarar da gwamatin tarayya kan mahimmancin da ke tattare da san ya mata manoma a daukacin fadin kasar nan a cikin shirye-shiyen aikin noma na kasar.

Wannan ankararwar ta fito ne daga bakin Hajiya Amina Jibrin ita ce, shugabar kungiyar mata manoma kanana da da ke a kasar nan.
A Jawabin da ta yi a kwanan baya a bikin ranar abinci ta duniya Hajiya Amina Jibrin ta bukaci da a tallafa wa manoman, musamman idana aka yi dubi da yadda iftila’in ambaliyar ruwan sama ta yiwa wasu manoman kasar nan barna a gonakansu, inda ta sanar da cewa, matan manoma musamman na bukatar tallafi domin su samu samar ci gaba da yin noman da kuma tsyawa da kafafunsu.

Shugabar ta ci gaba da cewa, ya zama wajibi mahukunta a kasar nan da su samar da dokokin da za su bayar da damar tallafa wa kananan manoma, musamman a dora su a kan yin inshorar aikin noma.

Hajiya Amina ta kuma shawarci gwamnatin jihar Bauchi ta kebe kanana manoman da ke a fadin jihar, bisa yarjejeniyar da aka sa wa hannu ta Maputo.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro

Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025
Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.