• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dinkin Duniya Ta Koka Kan Rashin Tallafa Wa Mata Manoma A Nijeriya

by Sulaiman and Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Ambaliyar Ruwa A Jihar Bayelsa Kalubale Ne Mai Girman Gaske – Majalisar Dinkin Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin wakiliyar mata a Majalisar dinkin duniya, Lansana Wonneh ya koka kan yadda mata manoma da ke a karkara a kasar nan, ba samun tallafin a kan Sana’ar ta su ta yin noma.

Ya sanar da cewa, matan manoma a karkara, na bayar da gagarumar gudunmawa,musamman wajen kara bunkasa samar da abinci da kuma kara habaka tattalin arzikin kasar nan.

  • Ambaliyar Ruwa: Manoma Sun Samu Tallafin Asusun Bunkasa Noma

Ya sanar da hakan ne a wani taro a garin Kalaba a kan bikin zagayowar ranar mata manoma da ke a karkara ta duniya, inda ya ci gaba da cewa, an shirya taron ne domin a kara wa matan manoma karkashin kokarin da suke yi na samar da wadataccen abinci, musamman mai gina jiki a daukacin fadin Nijeriya.

Wonneh ya ce an shirya taron ne domin zaburar da mata mazauna karkarar da ke kokarin samarwa, da sarrafawa, hadi da tattata abinci don ciyar da al’umma, duk da watsi da su da ake yi a kasar.
Ya ce Majalisar Dinkin Duniya za ta hada kai da Gwamnatin Nijeriya domin kawo gyara a lamarin.

“An shirya taron ne domin a kara wa matan manoma karkashin kokarin da suke yi na samar da wadataccen abinci, musamman mai gina jiki a daukacin fadin Nijeriya da kumakara karfafa masu gwiwa don su kara samar wa da kawunan su da kudaden shiga don sana’ar ta su ta kara bunkasa”.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

A cewar Wonneh ya zama wajibi matan manoman da ke a karkara a dinga tallafa mUsu, musamman idan aka yi dubi da irin wahalhalun da suke fuskanta a lokacin gudanar da aikin na su na noman.

Ya sanar da cewa, burin da majalisar ta ke da shi a kan matan manoman na karkara shine, aga suna samun kayan aikin noman, musamman na zamani da kuma samar masu da wadatattun kudade.

Ya yi nuni da cewa, tallafin zai taimaka masu matuka wajen kara mayar da hankali a kan gudanar da aikin na su na noman.
A wata sabuwa kuwa, an ankarar da gwamatin tarayya kan mahimmancin da ke tattare da san ya mata manoma a daukacin fadin kasar nan a cikin shirye-shiyen aikin noma na kasar.

Wannan ankararwar ta fito ne daga bakin Hajiya Amina Jibrin ita ce, shugabar kungiyar mata manoma kanana da da ke a kasar nan.
A Jawabin da ta yi a kwanan baya a bikin ranar abinci ta duniya Hajiya Amina Jibrin ta bukaci da a tallafa wa manoman, musamman idana aka yi dubi da yadda iftila’in ambaliyar ruwan sama ta yiwa wasu manoman kasar nan barna a gonakansu, inda ta sanar da cewa, matan manoma musamman na bukatar tallafi domin su samu samar ci gaba da yin noman da kuma tsyawa da kafafunsu.

Shugabar ta ci gaba da cewa, ya zama wajibi mahukunta a kasar nan da su samar da dokokin da za su bayar da damar tallafa wa kananan manoma, musamman a dora su a kan yin inshorar aikin noma.

Hajiya Amina ta kuma shawarci gwamnatin jihar Bauchi ta kebe kanana manoman da ke a fadin jihar, bisa yarjejeniyar da aka sa wa hannu ta Maputo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ganduje Ya Ware Naira Miliyan 300 A Matsayin Kudin Karatun Daliban Kano Da Ke Karatu A Waje

Next Post

Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro

Related

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

3 days ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

3 days ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

1 week ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

2 weeks ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

2 weeks ago
Next Post
Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro

Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun KuÉ“utar Da ‘Yan Ghana 19 Da Aka Yaudare Su Zuwa Nijeriya

July 8, 2025
ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A FaÉ—in Nijeriya

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A FaÉ—in Nijeriya

July 8, 2025
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato

July 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

July 8, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da ÆŠumi-ÆŠumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da ÆŠumi-ÆŠumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar HaÉ—aka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar HaÉ—aka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.