• English
  • Business News
Thursday, September 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar ECOWAS Ta Shirya Fara Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Dokoki

by Abubakar Sulaiman
4 hours ago
in Manyan Labarai
0
Majalisar ECOWAS Ta Shirya Fara Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Dokoki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Ƙungiyar Ƙasashen Yammacin Afrika (ECOWAS) ta bayyana shirin fara amfani da Fasahar AI na Wucin-Gadi (AI) domin inganta tasiri da inganta ayyukan dokoki a majalisar. Shugabar majalisar, Rt. Hon. Memounatou Ibrahima, ta sanar da haka a lokacin rufe taron bita na majalisar karo na biyu a 2025 da aka gudanar a birnin Fatakwal na Jihar Rivers, wanda taken sa shi ne: “Amfani da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Majalisa, Gwamnatin Da Cigaba a Yankin ECOWAS.”

Taron ya ɗauki kwanaki uku, inda masana suka gabatar da bayanai, aka gudanar da tattaunawa da mahawara kan muhimmancin wannan fasaha wajen tallafa wa ayyukan dokoki. An kuma jaddada buƙatar samar da ƙa’idojin da za su kare yankin daga haɗarin AI, musamman ganin ƙalubalen da ke tattare da ƙarancin ababen more rayuwa a Afrika ta Yamma.

  • ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000
  • ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

A jawabin da aka karanta a madadin shugabar, ta hannun mataimakinta na huɗu Billay Tunkara, an bayyana AI a matsayin “sauyin da ba za a iya samun ci gaba ba tare da shi ba”, inda aka ce cikin ƙanƙanin lokaci fasahar ta riga ta sauya tsarin tattalin arziƙi, da zamantakewa da mulki a yankin. Shugabar ta jaddada cewa idan aka sarrafa fasahar yadda ya kamata, za ta taimaka wajen samar da ingantattun dokoki, da tattaunawa mai ma’ana da kuma ƙarfafa ikon sa ido na majalisa.

Sai dai wasu ƴan majalisa sun nuna damuwa cewa fasahar na iya kawo barazana idan ba a yi amfani da ita yadda ya kamata ba. Duk da haka, an yi kira da a yi amfani da AI ta yadda za a ci gajiyar damar da take bayarwa ba tare da barin ta lalata ƙimomin ɗan Adam da tushen dimokuraɗiyya ba.

Taron bitar ya zama wani sabon mataki na haɗin gwuiwa a tsakanin ƙasashen ECOWAS don shigar da AI cikin ayyukan majalisa. A cewar shugabar, shawarwarin da aka tattara za su zama tubalin tsare-tsaren da za su tabbatar da cewa majalisar ta rungumi wannan sabuwar fasaha cikin nasara.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nemi A Bai Wa Nijeriya Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Ɗinkin Duniya 

UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASNigeriaRivers
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Sanar Da Gudummawar Kasarsa Dangane Da Tunkarar Sauyin Yanayi Nan Zuwa 2035

Next Post

Collins Whitworth Zai Kafa Tarihin Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

Related

Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nemi A Bai Wa Nijeriya Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Ɗinkin Duniya 

1 minute ago
UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro
Manyan Labarai

UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro

7 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane Biyu Da Laifin Garkuwa Da Wani Yaro Ɗan Shekara 10 A Neja

22 hours ago
Rashin Gyaran Hanya Ne Ya Haddasa Hatsarin Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna – NSIB
Manyan Labarai

Rashin Gyaran Hanya Ne Ya Haddasa Hatsarin Jirgin Ƙasan Abuja–Kaduna – NSIB

1 day ago
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mahara 2 A Anambra, Sun Kwato Makamai 
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutum 4,383, Sun Ceto 1,138 Daga Hannun Mahara Cikin Wata 3

1 day ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Kama Masu Laifi

1 day ago
Next Post
Collins Whitworth Zai Kafa Tarihin Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

Collins Whitworth Zai Kafa Tarihin Shiga Kundin 'Guinness World Record' Tare Da Goyon Bayan Indomie

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Ya Nemi A Bai Wa Nijeriya Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Ɗinkin Duniya 

September 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Kakkaɓe Masu Amfani da Takardun Bogi a Ma’aikatunta

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Kakkaɓe Masu Amfani da Takardun Bogi a Ma’aikatunta

September 25, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

September 25, 2025
Collins Whitworth Zai Kafa Tarihin Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

Collins Whitworth Zai Kafa Tarihin Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

September 25, 2025
Majalisar ECOWAS Ta Shirya Fara Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Dokoki

Majalisar ECOWAS Ta Shirya Fara Amfani Da Fasahar AI Don Inganta Ayyukan Dokoki

September 25, 2025
Xi Ya Sanar Da Gudummawar Kasarsa Dangane Da Tunkarar Sauyin Yanayi Nan Zuwa 2035

Xi Ya Sanar Da Gudummawar Kasarsa Dangane Da Tunkarar Sauyin Yanayi Nan Zuwa 2035

September 25, 2025
Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa

Ƴan Bindiga Sun Harbe Wanda Suka Sace Saboda Rashin Isassun Kuɗi A Asusunsa

September 25, 2025
Sin Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kai

Sin Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kai

September 25, 2025
Gwamna Radda Ya Nemi Taimako Don Gina Gidaje Ga Waɗanda Rikicin Ta’addanci Ya Shafa

Gwamna Radda Ya Nemi Taimako Don Gina Gidaje Ga Waɗanda Rikicin Ta’addanci Ya Shafa

September 25, 2025
UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro

UNGA: Tinubu Ya Nemi Kujerar Dindindin Ga Nijeriya A Majalisar Tsaro

September 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.