• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

by Abubakar Sulaiman
2 hours ago
in Tattalin Arziki
0
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin Majalisar Wakilai kan Albarkatun Man Fetur ya bayyana cewa zai shiga tsakani domin warware rikicin da ke tsakanin Kamfanin Dangote da Ƙungiyar Ma’aikatan Man Fetur da Gas (NUPENG), don tabbatar da zaman lafiya da daidaito a harkar man fetur a ƙasar nan.

Wannan mataki ya biyo bayan taron kwana uku da aka gudanar a Legas, inda ƴan majalisa, da hukumomi da masu ruwa da tsaki a masana’antar suka tattauna kan matsalolin da ke ci gaba da damun sashen mai na ƙasa. Shugaban kwamitin, Hon. Ikenga Imo Ugochinyere, ya shaida wa manema labarai cewa kwamitin ba zai bari rikici tsakanin manyan masu saka jari da ƙungiyoyin kwadago ya samu tangarɗa ba.

  • Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
  • Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

“Babban burinmu shi ne kawo sauye-sauyen da za su tabbatar da inganci, da adalci da gasa mai kyau ga kowa. Za mu shiga tsakani don tabbatar da cewa babu wani ɓangare da zai ji an tauye masa haƙƙinsa,” in ji shi. Ya ƙara da cewa kwamitin ya damu da matsalolin samar da ɗanyen mai da ke kawo cikas ga masana’antar.

Haka kuma, taron ya sake nazarin ce-ce-ku-ce kan yadda Kamfanin NNPC Limited ya karɓi kadarorin OVH Energy. Ugochinyere ya tabbatar da cewa bincike na musamman kan wannan ciniki ya kai matakin ƙarshe, wanda ya bambanta da binciken farko da aka yi watsi da shi a zauren majalisar. Duk da cewa wasu masu ruwa da tsaki ba su miƙa takardunsu ba, ya ce kwamitin zai ci gaba da aikinsa domin cika alƙawarin majalisar.

Ƴan majalisa sun yaba da ƙoƙarin Hukumar NMDPRA, da tashar Tace Mai ta Dangote, da sauran masu zuba jari a fannin, tare da lura da cigaba da ake samu wajen gyaran tashar tace mai ta Fatakwal. Rahotannin ƙananan kwamitoci da aka kafa a taron za su fito nan gaba kaɗan, kuma za su zama tubalin dokokin majalisa kan rabon ɗanyen mai, da sabunta matatun mai da kuma inganta tsarin sa ido.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Sauye-Sauyen Da Aka Yi A Fannin Mai Da Iskar Gas Suka Samar Da Gagarumin Ci Gaba A Wannan Shekarar

Manyan Motoci 2,000 A Kullum Ke Zirga-zirga A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas —Rahoto


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DangotemajalisaNUPENGReps
ShareTweetSendShare
Previous Post

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

Next Post

Uba Sani Ya Jagoranci Yunƙurin Ƙara Yawan Rajistar Masu Zaɓe a Jihar Kaduna

Related

Yadda Sauye-Sauyen Da Aka Yi A Fannin Mai Da Iskar Gas Suka Samar Da Gagarumin Ci Gaba A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Yadda Sauye-Sauyen Da Aka Yi A Fannin Mai Da Iskar Gas Suka Samar Da Gagarumin Ci Gaba A Wannan Shekarar

1 day ago
Manyan Motoci 2,000 A Kullum Ke Zirga-zirga A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas —Rahoto
Tattalin Arziki

Manyan Motoci 2,000 A Kullum Ke Zirga-zirga A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas —Rahoto

1 day ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Tattalin Arziki

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

2 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

3 weeks ago
tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

4 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

4 weeks ago
Next Post
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Uba Sani Ya Jagoranci Yunƙurin Ƙara Yawan Rajistar Masu Zaɓe a Jihar Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

September 27, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Uba Sani Ya Jagoranci Yunƙurin Ƙara Yawan Rajistar Masu Zaɓe a Jihar Kaduna

September 27, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

Majalisar Shura ta Kano Za Ta Binciki Zargin Batanci Ga Annabi Kan Malam Triumph

September 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

September 27, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

September 27, 2025
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

September 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.