• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malamai Suna Takara Da ’Yan Siyasa Wajen Neman Mulki –Sule Lamido

by Yusuf Shuaibu
8 months ago
Takara

Tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana damuwarsa kan yadda malaman addini ke ci gaba da shiga harkokin siyasa, inda ya bayyana cewa malaman addini a yanzu suna da tasirin gaske kan masu zabe da kuma harkokin siyasa.

Lamido ya bayyana hakan ne a cikin wani faifan bidiyo da aka watsa a lokacin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga Sheikh Yusuf Sambo Rigachikun a Kaduna sakamakon rasuwar babban dansa.

  • Khalifan Sheikh Ibrahim Inyas Daga Ƙasar Sanigal Ya Goyi Bayan Sunusi Lamido Sunusi II
  • Duk Wanda Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani, Shi Ma Sai An Hukunta Shi – Gwamna Sule 

Tsohon gwamnan Jigawan ya koka da yadda malaman addini suka mamaye fagen siyasa, inda suka fito karara suna kamfen ga ‘yan takara tare da jagorantar mabiyansu kan wadanda za su mara wa baya.

“Duk da albarkar da malaman addini suke da ita, amma a yanzu malaman addini suna kokawar neman mulki. Ya kamata malamai su zama masu kulawa da ’yan siyasa, amma tun da suna son mulki, mu ’yan siyasa mun yanke shawarar komawa gefe mu zuba ido. Muna jiran su fada mana wanda za mu zaba bisa ga burinsu. Domin samun daidaito da adalci, ya kamata kowa ya kiyaye matsayinsa a cikin al’umma,” in ji shi.

Lamido ya bayyana cewa, kamar yadda jam’iyyun siyasa ke fama da rikicin cikin gida, su ma kungiyoyin addini na fuskantar rarrabuwar kawuna, inda ya yi gargadin cewa yanayin siyasar Nijeriya zai kasance cikin rudani matukar ba a samu hadin kai ba.

LABARAI MASU NASABA

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Idan za a iya tunawa dai, malaman addini sun taka rawa wajen zaburar da jama’arsu domin yin rajistar masu zabe. Duk da haka, a babban zaben 2023 wanda yana daya daga cikin mafi zaben da ya janyo rarrabuwar kawuna a Nijeriya, masallatai da coci-coci sun taka rawar gani wajen tursasa mabiyansu su zabi nasu ‘yan takara.

Mafi yawancin wa’azi da khudubobi sun kasance wurin tattauna harkokin siyasa. A wasu majami’u, fastoci sun yi da’awar manzancin kan ‘yan takararsu, yayin da a cikin malaman addinin musulmi, limamai sun bukaci mabiya da su yi zabe ta hanyar addini. Abin mamaki, yawancin wadannan hasashen addini ba su tabbata ba.

A kwann nan dai an tafka cece-kuce kan taron da aka shirya gudanarwa a ranar 22 ga watan Fabrairun 2025 a Abuja, wanda ake sa ran za a hada mahardata alkur’ani har 30,000. An dage taron ne ba tare da saka wani lokaci ba, sakamakon kalubalantar lamarin da wasu malaman addinin Islama suka nuna, inda suka nuna shakku kan sahihancinsa tare da zargin cewa wani yunkuri ne na siyasa gabanin zaben shugaban kasa na 2027.

Idn za a iya tunawa dai, tikitin tsayawa takarar shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu na Musulmi-musulmi a shekarar 2023, wanda kusan ya wargaje tsarin fagen siyasa, a karshe ya tsira saboda gagarumin goyon baya daga malaman addini da suka tabbatar wa mabiyansu. Shi ma kabilanci da bangarenci, musamman a kudu maso yamma ya taka rawar gani.

A lokacin zaben 2023, abokan Tinubu a arewacin Nijeriya sun yi zawarcin manyan malaman ddinin Musulunci, inda suka samu goyon bayansu. Yanzu, da alama ana ci gaba da yin irin wannan kokarin, yayin da ‘yan wasan siyasa suka fara dabarun lashe zabe a 2027.

A daya hannun kuma, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ana kyautata zaton zai sake dauko abokin takararsa daga yankin arewacin kasar da galibinsu musulmai ne a zabe mai zuwa. Kasancewarsa yana halartar tarukan da suka shafi addinin Musulunci, ana kallonsa a matsayin wanda yake kokari wajen jawo hankalin malaman addini domin samun nasara.

Magoya bayan Obi sun ce baya ga zargin tafka magudin zaben da kuma gazawarsa wajen shigar da shugabannin addini a arewacin kasar ya taimaka matuka gaya wajen rashin nasararsa a 2023. Yayin da zaben 2027 ke gabatowa, da alama magoya bayansa sun kudiri aniyar kauce wa kuskuren da suka yi a zaben da ya gabata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina
Labarai

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
Labarai

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025
Next Post
Babu Wani Abin Burgewa A APC, Za Mu Kori Wannan Gwamnati A 2027 – Tambuwal

Babu Wani Abin Burgewa A APC, Za Mu Kori Wannan Gwamnati A 2027 – Tambuwal

LABARAI MASU NASABA

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025
An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

October 27, 2025
Takara

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.