• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malaman Kano Sun Roki Tinubu Ya Bari A Yi Sulhu Kan Rikicin Masarautar Jihar 

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Malaman Kano Sun Roki Tinubu Ya Bari A Yi Sulhu Kan Rikicin Masarautar Jihar 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Malaman addinin Musulunci a Jihar Kano sun yi kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da ya bai wa al’ummar jihar damar magance rikicin masarautar ba tare da amfani da karfin iko ba. 

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da jami’an tsaro ke ci gaba da kokarin samar da zaman lafiya a jihar.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Fara Gina Gidaje Masu Saukin Kudi 1,250 A Jihohi Hudu
  • Jami’an Tsaro Na Ganawar Sirri Da Abba Da Sarki Sanusi II A Fadar Kano

Malaman sun bayyana matukar damuwarsu dangane da tashe-tashen hankulan da ke faruwa a masarautar, inda suka bukaci Gwamnatin Tarayya da ta sa baki domin wanzuwar zaman lafiya.

A cikin wata sanarwa da Shaikh Abdullahi Uwais Limanci ya sanya wa hannu, malaman sun yi gargadin cewa lamarin na iya haifar da tashin-tashina.

Sanarwar ta kara da cewa “Jihar Kano na daya daga cikin jihohin da aka fi samun zaman lafiya a Nijeriya duk da sarkakiyar siyasarta, ya zama wajibi shugaba Bola Ahmed Tinubu ya dauki dukkan matakan da suka dace domin wanzar da zaman lafiya a jihar.”

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Malaman sun jaddada muhimmancin barin al’ummar Kano wajen warware matsalolinsu cikin ruwan sanyi, ba tare da yin amfani da karfi ba wanda a cewarsu hakan zai iya haifar da asarar rayuka.

Sun bayyana muhimmancin tattaunawa da mutunta juna wajen tunkarar rikicin da ke faruwa a yanzu.

“Muna kira ga mai girma shugaban kasa da ya bai wa al’ummar Jihar Kano damar magance wadannan matsaloli cikin ruwan sanyi ba tare da yin amfani da karfi da zai kai ga asarar rayuka da dukiyoyi ba.

Gammayar kungiyar malaman ta kuma yi kira ga bangarorin sarakunan da ke rikici da juna da su yi amfani da hanyoyi da suka dace don sim zaman lafiya a tsakaninsu.

Malaman sun yi alkawarin shiga tsakani tare da tuntubar duk bangarorin da abin ya shafa don samar da mafita cikin lumana.

A halin yanzu dai al’amura sun fara daidaita a jihar, bayan da shugaban hukumomin tsaro a jihar suka gana da duka bangarorin biyu da suka hada da tsagin sabon Sarki Sanusi Lamido II wanda ke samun goyon bayan gwamnati mai ci.

Sai kuma tsagin tsohon Sarki Aminu Ado Bayero, wanda wasu rahotanni suka bayyana yana samun goyon baya daga sama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaAminu Ado BayerokanoRikicin MasarautaSanusi II
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Gina Gidaje Masu Saukin Kudi 1,250 A Jihohi Hudu

Next Post

Bankin TAJBank Ya Sake Lashe Kambun Gwarzon Bankin Musulunci A Nijeriya

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

43 minutes ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

8 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

10 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

11 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

20 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

23 hours ago
Next Post
Bankin TAJBank Ya Sake Lashe Kambun Gwarzon Bankin Musulunci A Nijeriya

Bankin TAJBank Ya Sake Lashe Kambun Gwarzon Bankin Musulunci A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

August 22, 2025
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

August 22, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

August 22, 2025
Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

August 22, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

August 22, 2025
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

August 22, 2025
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar Nan (7)

August 22, 2025
An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

August 22, 2025
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

August 22, 2025
Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci Bunkasa Fannin Mai Da Ake Hakowa A Teku

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.