ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Sin

Al’ummar yankin Latin Amurka sun shiga wannan mako da kafar dama, biyo bayan manufar gwajin da kasar Sin ta fara aiwatarwa a ranar Lahadin da ta gabata, na ba ’yan kasashen Brazil da Argentina da Chile da Peru da ma Uruguay, damar shigowa kasar ba tare da biza ba har na tsawon kwanaki 30, domin gudanar da harkokin da suka shafi kasuwanci da ziyara da bude ido da yada zango ko kuma harkokin da suka shafi al’adu. 

Babu makawa, duk abun da kasar Sin ta furta, to da gaske take. Kuma duk burin da ta sanya a gaba, za ta dage wajen kai wa ga cimma masa. Cikin rahoton aikin gwamnati da aka fitar yayin manyan taruka biyu da aka yi a watan Maris na bana, gwamnatin kasar Sin ta nanata niyyarta ta fadada bude kofa, tana cewa ba tare da la’akari da duk wani sauyi da duniya za ta tsinci kanta ciki ba, Sin za ta ci gaba da bude kofarta ga kasashen waje. Wannan ya nuna muradin kasar Sin na ganin kasashen duniya sun samu ci gaba na bai daya da inganta huldar tsakanin sassan duniya da ma goyon bayanta ga dunkulewar tattalin arzikin duniya.

  • Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya
  • Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

A yanayin da aka shiga a duniya, babu wata kasa ko al’umma da za ta kebe kanta ita kadai ko rufe kofarta, sannan ta yi tsammanin samun ci gaba ko fifiko kan sauran kasashe. Kulle kofa da wasu kasashe ke son yi, ba zai kai ga muradin da ake son cimmawa na tabbatar da zaman lafiya da habakar tattalin arzikin duniya ba. Mun gani a baya-bayan nan, yadda harkokin cinikayya da tsarin samar da kayayyaki suka hargitse biyo bayan ra’ayin kariya da neman iko.

ADVERTISEMENT

Galibin matsalolin da ake samu tsakanin kasa da kasa da al’ummomin duniya, ya samo asali ne daga rashin fahimta ko yaduwar karairayi, amma cudanyar kasa da kasa da al’ummominsu ta hanyar bude kofa da maraba da juna, zai kara ba da damar fahimta da warware gaskiya da karya, ta yadda za a kai ga inganta fahimtar juna. Wannan na nuna cewa, bude kofa bai tsaya ga amfanawa bangaren tattalin arziki da cinikayya ba kadai, ya kai ga daukaka zaman lafiya da kyautata zamantakewa da samun ci gaba da samar da aikin yi da wayewar kai da kirkire-kirkire da sauransu.

Zuwa yanzu, matakin Sin game da bizar a bana, bai tsaya kan kasashen Latin Amurka ba, su ma ’yan kasashen Saudiyya da Oman da Kuwait da Bahrain, za su more wannan dama daga ranar 9 ga watan nan, har zuwa 8 ga watan Yunin 2026. Haka kuma, an fadada tsarin yada zango na tsawon sa’o’i 240 ga matafiya daga kasashe 54 ba tare da biza ba.

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Irin manufar bude kofa da gyare-gyare ta kasar Sin duniya da jama’arta suka fi bukata, domin ita ce za ta bada damar samun dunkulewar duniya da ci gabanta kamar yadda ake fata, har ma da kai wa gina duniya mai kyakkyawar makoma ga dukkannin dan adam. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

LABARAI MASU NASABA

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.