• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Ayyukan Tasoshin Teku Da Aka Watsar A Nijeriya…

Mun wallafa a ranar 28 ga Yuli, 2023

by Bello Hamza
2 years ago
in Rahotonni
0
Manyan Ayyukan Tasoshin Teku Da Aka Watsar A Nijeriya…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekaru bayan kaddamar da shirin samar da tasoshin teku na kan-tudu a sassan kasar nan har zuwa yanzu da dama daga cikinsu ba su fara aiki ba, ballantana a fara cin gajiyar su.

Binciken da LEADERSHIP ta yi, ya nuna cewa, tashar teku ta kan-tudun da aka samar a wasu jihohin kasar suna nan sun lalace bayan da aka narka biliyoyin naira don tabbatar da aikin ya samu nasarar da ake bukata.

  • Harin Filato: Gwamnati Ba Za Ta Huta Ba Har Sai An Hukunta Maharan – Shettima 
  • Ganduje Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Na’Abba

A yawancin garuruwan da aka kafa wadannan tasoshin tekunan an yi wa dubban matasan yankin alkawarin samun ayyukan yi wanda har zuwa yanzu babu wani fata na yiwuwar hakan. Haka kuma an lasa wa al’ummar yankunan zuma a baki a kan bunkasar tattalin arziki da ingantuwar rayuwa.

Gwamnatocin jihohin Kano, Katsina, Kaduna, Borno, Filato da Oyo sun samar da dubban hektoci na filaye ga gwamnatin tarayya amma saboda tsananin rashin cikakken shiri da gudanar da aiki tare tsakanin gwamnatocin jihohin da ma’aikatun gwamnatin tarayya da suke da hannu a kan lamarin har zuwa yanzu ba a kai ga samun nasarar da ake bukakata ba a kan shirin.

A watan Maris na shekarar 2006 ne majalisar zartaswar gwamnatin tarayya ta amince da a samar da tasoshin teku na kan-tudu a sassa 6 na tarayya Nijeriya wadanda suka hada da Isiala-Ngwa a Jihar Abiya; Erunmu Ibadan – a Jihar Oyo; Heipang Jos – a Jihar Filato; Funtuwa- a Jihar Katsina; Maiduguri –  a jihar Borno da kuma Dala a Jihar Kano.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Amma kuma tashar kan-tudu ta Kaduna da ba a sa a cikin tsarin farko na guda shida da aka yi shekarar 2006 ba, ta samu tagomashin kaddamarwar gwamnatin tarayya a shekarar 2018, an kuma yi haka ne don ya zama wurin da za a rika sauke kayayyakin da suka nufi kasashen da ba su da tasoshin ruwa da ke makwabtaka da Nijeriya kamar kasashen Nijar da Chadi, ta haka za a samu sakin safarar kayayyaki a tsakanin kasashen.

Tashar kan-tudu ta Kaduna ta fara gabatar da kwaryakwaryar aiki amma rashin kammala aikin hanyar jirgi yana kawo cikas ga zirga-zirgar kayayyaki daga tasoshin ruwan Nijeriya zuwa tashar kan-tudu ta Kaduna, kamar yadda bincike ya nuna.

Wakilinmu da ya ziyarci tashar ta Kaduna da ke unguwar Kakuri kusa da tashar jirgin kasa, inda ya lura da cewa wasu manyan motoci kalilan ake iya gani suna dauka da sauke kayayyaki a tashar a rana.

An kiyasta tashar na da karfin mu’amala da kayyakin da suka kai tan 29,000 a duk shekara, sannan za ta kuma iya samar da ayyukan yi ga mutum fiye da 5000.

A jihar Filato kuma, shekara 17 bayan kadamar da tashar kan-tudu na Heipang, da ke karamar hukumar Barikin Ladi da tsohon shugaban kasa, Janar Yakubu Gowon (mai ritaya), ya yi har yanzu ba a fara wani aiki a tashar ba.

Haka kuma a watan Fabrairu na shekarar 2023 ne gwamnatin tarayya ta kaddamar da tashar kan-tudu da ke Funtuwa a Jihar Katsina, inda ake sa ran ta zama masaukin manyan kayayyaki da kwantainonin da aka shirya fitarwa zuwa kasashen waje.

Tun bayan kaddamar da tashar har zuwa yanzu ba a kai ga fara aiki a tashar ba, ministan sufuri, Mu’azu Jaji Sambo ya jagoranci kaddamar da tashar.

Binciken da wannan jaridar ta yi ya nuna cewa, tashar na nan ba a aikin komai, sai da an fahimci wasu sun manyar da tashar wajen ajiye kayayyaki zuwa wani lokaci su kwashe abin su, duk kokarin da wakilinmu ya yi don jin ta bakin shugaban tashar ya ci tura.

Haka kuma a watan Agusta na shekarar 2022, gwamnatin tarayya ta kaddamar da tashar kan-tudu ta Kano da ke Dala, don ta kasance wurin saukar da kayayyaki da suka fito daga tasoshin Ruwan Nijeriya.

…Tashar Baro Ba Labari, Ciyayi Sun Mamaye, Ruwa Na Raruke Gabar Kogin

Ciyayi da sauran tsirrai suka mamaye tashar jiragen ruwa na biliyoyin naira a garin Baro ta Jihgar Neja wanda tsohon shhugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a shekarar 2019. A halin yanzu ma ruwa na ci gaba da cin gabar kogin har ya fara neman isa gine-ginen da aka yi na tashar.

Binciken da LEADERSHIP ta gudanar ya nuna cewa, gine-ginen da aka yi na tashar da sauran ayyukan da kwararru suka samar ya lakume wa gwamnatin tarayya naira biliyan 3.5, wannan bai hada da kudin yashe kogin ba don ba a sanya shi ba a ciki a lokacin da aka kaddamar da aikin.

Binciken ya kara nuna cewa, ciyawa da sauran tsirrai sun mamaye harabar tashar ce saboda tun da aka kaddamar da tashar ba a yi wani aiki ko guda daya ba a wurin duk kuwa da cewa, gwamnati ta yi alkawarin gudanar da aiki nan take a tashar a yayin kaddamarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Gana Da Jakadun Kasar Sin Dake Kasashen Waje Wadanda Suka Dawo Beijing Don Halartar Taro

Next Post

Samar Da Tsaro: Ribadu Ya Yaba Wa Sarakunan Gargajiya A Adamawa

Related

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

3 days ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

4 days ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

2 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

2 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

2 weeks ago
Next Post
Samar Da Tsaro: Ribadu Ya Yaba Wa Sarakunan Gargajiya A Adamawa

Samar Da Tsaro: Ribadu Ya Yaba Wa Sarakunan Gargajiya A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

July 29, 2025
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

July 29, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

July 29, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.