ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Ayyukan Tasoshin Teku Da Aka Watsar A Nijeriya…

Mun wallafa a ranar 28 ga Yuli, 2023

by Bello Hamza
2 years ago
Teku

Shekaru bayan kaddamar da shirin samar da tasoshin teku na kan-tudu a sassan kasar nan har zuwa yanzu da dama daga cikinsu ba su fara aiki ba, ballantana a fara cin gajiyar su.

Binciken da LEADERSHIP ta yi, ya nuna cewa, tashar teku ta kan-tudun da aka samar a wasu jihohin kasar suna nan sun lalace bayan da aka narka biliyoyin naira don tabbatar da aikin ya samu nasarar da ake bukata.

  • Harin Filato: Gwamnati Ba Za Ta Huta Ba Har Sai An Hukunta Maharan – Shettima 
  • Ganduje Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Na’Abba

A yawancin garuruwan da aka kafa wadannan tasoshin tekunan an yi wa dubban matasan yankin alkawarin samun ayyukan yi wanda har zuwa yanzu babu wani fata na yiwuwar hakan. Haka kuma an lasa wa al’ummar yankunan zuma a baki a kan bunkasar tattalin arziki da ingantuwar rayuwa.

ADVERTISEMENT

Gwamnatocin jihohin Kano, Katsina, Kaduna, Borno, Filato da Oyo sun samar da dubban hektoci na filaye ga gwamnatin tarayya amma saboda tsananin rashin cikakken shiri da gudanar da aiki tare tsakanin gwamnatocin jihohin da ma’aikatun gwamnatin tarayya da suke da hannu a kan lamarin har zuwa yanzu ba a kai ga samun nasarar da ake bukakata ba a kan shirin.

A watan Maris na shekarar 2006 ne majalisar zartaswar gwamnatin tarayya ta amince da a samar da tasoshin teku na kan-tudu a sassa 6 na tarayya Nijeriya wadanda suka hada da Isiala-Ngwa a Jihar Abiya; Erunmu Ibadan – a Jihar Oyo; Heipang Jos – a Jihar Filato; Funtuwa- a Jihar Katsina; Maiduguri –  a jihar Borno da kuma Dala a Jihar Kano.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Amma kuma tashar kan-tudu ta Kaduna da ba a sa a cikin tsarin farko na guda shida da aka yi shekarar 2006 ba, ta samu tagomashin kaddamarwar gwamnatin tarayya a shekarar 2018, an kuma yi haka ne don ya zama wurin da za a rika sauke kayayyakin da suka nufi kasashen da ba su da tasoshin ruwa da ke makwabtaka da Nijeriya kamar kasashen Nijar da Chadi, ta haka za a samu sakin safarar kayayyaki a tsakanin kasashen.

Tashar kan-tudu ta Kaduna ta fara gabatar da kwaryakwaryar aiki amma rashin kammala aikin hanyar jirgi yana kawo cikas ga zirga-zirgar kayayyaki daga tasoshin ruwan Nijeriya zuwa tashar kan-tudu ta Kaduna, kamar yadda bincike ya nuna.

Wakilinmu da ya ziyarci tashar ta Kaduna da ke unguwar Kakuri kusa da tashar jirgin kasa, inda ya lura da cewa wasu manyan motoci kalilan ake iya gani suna dauka da sauke kayayyaki a tashar a rana.

An kiyasta tashar na da karfin mu’amala da kayyakin da suka kai tan 29,000 a duk shekara, sannan za ta kuma iya samar da ayyukan yi ga mutum fiye da 5000.

A jihar Filato kuma, shekara 17 bayan kadamar da tashar kan-tudu na Heipang, da ke karamar hukumar Barikin Ladi da tsohon shugaban kasa, Janar Yakubu Gowon (mai ritaya), ya yi har yanzu ba a fara wani aiki a tashar ba.

Haka kuma a watan Fabrairu na shekarar 2023 ne gwamnatin tarayya ta kaddamar da tashar kan-tudu da ke Funtuwa a Jihar Katsina, inda ake sa ran ta zama masaukin manyan kayayyaki da kwantainonin da aka shirya fitarwa zuwa kasashen waje.

Tun bayan kaddamar da tashar har zuwa yanzu ba a kai ga fara aiki a tashar ba, ministan sufuri, Mu’azu Jaji Sambo ya jagoranci kaddamar da tashar.

Binciken da wannan jaridar ta yi ya nuna cewa, tashar na nan ba a aikin komai, sai da an fahimci wasu sun manyar da tashar wajen ajiye kayayyaki zuwa wani lokaci su kwashe abin su, duk kokarin da wakilinmu ya yi don jin ta bakin shugaban tashar ya ci tura.

Haka kuma a watan Agusta na shekarar 2022, gwamnatin tarayya ta kaddamar da tashar kan-tudu ta Kano da ke Dala, don ta kasance wurin saukar da kayayyaki da suka fito daga tasoshin Ruwan Nijeriya.

…Tashar Baro Ba Labari, Ciyayi Sun Mamaye, Ruwa Na Raruke Gabar Kogin

Ciyayi da sauran tsirrai suka mamaye tashar jiragen ruwa na biliyoyin naira a garin Baro ta Jihgar Neja wanda tsohon shhugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a shekarar 2019. A halin yanzu ma ruwa na ci gaba da cin gabar kogin har ya fara neman isa gine-ginen da aka yi na tashar.

Binciken da LEADERSHIP ta gudanar ya nuna cewa, gine-ginen da aka yi na tashar da sauran ayyukan da kwararru suka samar ya lakume wa gwamnatin tarayya naira biliyan 3.5, wannan bai hada da kudin yashe kogin ba don ba a sanya shi ba a ciki a lokacin da aka kaddamar da aikin.

Binciken ya kara nuna cewa, ciyawa da sauran tsirrai sun mamaye harabar tashar ce saboda tun da aka kaddamar da tashar ba a yi wani aiki ko guda daya ba a wurin duk kuwa da cewa, gwamnati ta yi alkawarin gudanar da aiki nan take a tashar a yayin kaddamarwar.

Teku
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Samar Da Tsaro: Ribadu Ya Yaba Wa Sarakunan Gargajiya A Adamawa

Samar Da Tsaro: Ribadu Ya Yaba Wa Sarakunan Gargajiya A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.