• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Jami’an Sin Sun Gana Da Tsohon Sakataren Harkokin Wajen Amurka Henry Kissinger

by CMG Hausa
2 years ago
Sin

Yau Laraba 19 ga wata, mamba a ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kuma daraktan ofishin lura da harkokin kasashen waje na kwamitin kolin Wang Yi, ya gana da tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Henry Kissinger a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Yayin ganawar ta su Wang ya bayyana cewa, manufofin kasar Sin ga Amurka na da alaka da juna, wadanda ke kan ka’idojin girmama juna, da kasancewa cikin yanayi na zaman lafiya, da hadin kai don samun nasara tare, kamar yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar.

  • Sin Na Ganin Karuwar Sabbin Kamfanonin Kasashen Waje A Kasar

Wadannan ka’idoji sun kasance hanya mai dacewa, ta raya dangantaka tsakanin manyan kasashen biyu wato Sin da Amurka. Kaza lika kasar Sin na da karfin kara samun bunkasuwa, hakan kuma na bin yanayin ci gaban tarihi. Kuma ba zai yiwu a yi yunkurin canja hanyar ci gaban Sin ba, haka kuma ba zai yiwu a nemi hana ci gaban Sin ba.

A nasa bangaren, Mr. Kissinger ya furta cewa, Amurka da Sin kasashe ne da ke da babban tasiri a duniya. Batun tabbatar da raya dangantaka a tsakanin bangarorin biyu yadda ya kamata, na da nasaba da cimma nasarar zaman lafiya, da kwanciyar hankali, da alfanun al’ummomin duniya baki daya.

Kissinger ya kara da cewa, komin wahalhalun da suke fuskanta, ya kamata bangarorin biyu su nuna wa juna daidaito, da kiyaye tuntubar juna. Ya ce ba za a amince da a nuna wa juna wariya ba. Kuma kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, alkawari ne da kasar Amurka ta yi a cikin Sanarwar Shanghai da aka fitar a shekarar 1972. Kuma an yi imanin cewa ba za a canza da karya wannan alkawari ba.

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Ban da haka kuma, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin, kana ministan tsaron kasar janar Li Shangfu ya gana da Kissinger yau a Beijing.

Li ya ce, a wannan duniya mai cike da rudani da sauye-sauye, jama’ar dukkan kasashe suna fatan Sin da Amurka za su sauke nauyin da ke wuyansu a matsayinsu na manyan kasashe, tare da kiyaye wadata da kwanciyar hankali a duniya baki daya.

Li ya bayyana fatan cewa, Amurka za ta yi aiki tare da kasar Sin wajen aiwatar da ra’ayin da shugabannin kasashen biyu suka cimma, da sa kaimi ga bunkasuwar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da sojojinsu.

Kissinger, a nasa bangaren ya ce a duniya ta yau, kalubale da damammaki suna cudanya, don haka ya kamata Amurka da Sin su kawar da rashin fahimtar juna, su zauna tare cikin lumana, da kuma kaucewa fada.

Ya bayyana fatan bangarorin biyu za su yi amfani da hikima, da yin duk wani kokari na samar da sakamako mai kyau don raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya. (Kande Gao &Yahaya Babs)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
Next Post
Kakakin Majalisar Wakilai Ya Ta Ya Musulmi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Musulunci Ta 1445

Kakakin Majalisar Wakilai Ya Ta Ya Musulmi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Musulunci Ta 1445

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.