ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Jami’an Sin Sun Gana Da Tsohon Sakataren Harkokin Wajen Amurka Henry Kissinger

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Yau Laraba 19 ga wata, mamba a ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kuma daraktan ofishin lura da harkokin kasashen waje na kwamitin kolin Wang Yi, ya gana da tsohon sakataren harkokin wajen kasar Amurka Henry Kissinger a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Yayin ganawar ta su Wang ya bayyana cewa, manufofin kasar Sin ga Amurka na da alaka da juna, wadanda ke kan ka’idojin girmama juna, da kasancewa cikin yanayi na zaman lafiya, da hadin kai don samun nasara tare, kamar yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar.

  • Sin Na Ganin Karuwar Sabbin Kamfanonin Kasashen Waje A Kasar

Wadannan ka’idoji sun kasance hanya mai dacewa, ta raya dangantaka tsakanin manyan kasashen biyu wato Sin da Amurka. Kaza lika kasar Sin na da karfin kara samun bunkasuwa, hakan kuma na bin yanayin ci gaban tarihi. Kuma ba zai yiwu a yi yunkurin canja hanyar ci gaban Sin ba, haka kuma ba zai yiwu a nemi hana ci gaban Sin ba.

ADVERTISEMENT

A nasa bangaren, Mr. Kissinger ya furta cewa, Amurka da Sin kasashe ne da ke da babban tasiri a duniya. Batun tabbatar da raya dangantaka a tsakanin bangarorin biyu yadda ya kamata, na da nasaba da cimma nasarar zaman lafiya, da kwanciyar hankali, da alfanun al’ummomin duniya baki daya.

Kissinger ya kara da cewa, komin wahalhalun da suke fuskanta, ya kamata bangarorin biyu su nuna wa juna daidaito, da kiyaye tuntubar juna. Ya ce ba za a amince da a nuna wa juna wariya ba. Kuma kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, alkawari ne da kasar Amurka ta yi a cikin Sanarwar Shanghai da aka fitar a shekarar 1972. Kuma an yi imanin cewa ba za a canza da karya wannan alkawari ba.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Ban da haka kuma, mamban majalisar gudanarwar kasar Sin, kana ministan tsaron kasar janar Li Shangfu ya gana da Kissinger yau a Beijing.

Li ya ce, a wannan duniya mai cike da rudani da sauye-sauye, jama’ar dukkan kasashe suna fatan Sin da Amurka za su sauke nauyin da ke wuyansu a matsayinsu na manyan kasashe, tare da kiyaye wadata da kwanciyar hankali a duniya baki daya.

Li ya bayyana fatan cewa, Amurka za ta yi aiki tare da kasar Sin wajen aiwatar da ra’ayin da shugabannin kasashen biyu suka cimma, da sa kaimi ga bunkasuwar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da sojojinsu.

Kissinger, a nasa bangaren ya ce a duniya ta yau, kalubale da damammaki suna cudanya, don haka ya kamata Amurka da Sin su kawar da rashin fahimtar juna, su zauna tare cikin lumana, da kuma kaucewa fada.

Ya bayyana fatan bangarorin biyu za su yi amfani da hikima, da yin duk wani kokari na samar da sakamako mai kyau don raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya. (Kande Gao &Yahaya Babs)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Kakakin Majalisar Wakilai Ya Ta Ya Musulmi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Musulunci Ta 1445

Kakakin Majalisar Wakilai Ya Ta Ya Musulmi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Musulunci Ta 1445

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.