• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Makaratun Jihar Bauchi Sun Ayyana Yajin Aikin Gargadi Na Mako 2

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Manyan Makaratun Jihar Bauchi Sun Ayyana Yajin Aikin Gargadi Na Mako 2
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamitin hadaka na manyan makaratun guda biyar da ke jihar Bauchi (JAC), sun ayyana tafiya yajin aikin jan kunne na tsawon kwanaki 14 da zai fara aiki daga ranar Laraba 19 ga watan Yuli zuwa ranar Lahadi 30 ga watan Yulin 2022 domin jawo hankalin Gwamnatin jihar Bauchi da ta share musu hawayensu.

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida a wani taron da suka kira, Shugaban JAC, Abdulkadir Mohammed, ya ce bukatun da suke da su, sun kunshi a gaggauta biyan albashin dukkanin mambobin kungiyar ke bi ba tare da bata wani lokaci ba.

  • 2023: Muna Fata APC Ta Dawo Mulki A Jihar Bauchi -Kwamared Sabo

Wakilinmu ya nakalto cewa hadakar makaratun sun hada da Kwalejin ilimi ta Adamu Tafawa Balewa da ke Kangere da Kwalejin ilimi, koyar da ilimin shari’a da sashin ilimin komai da ruwanka ta A.D Rufa’i da ke Misau da Kwalejin ilimi ta Aminu Saleh da ke garin Azare da Kwalejin Ilimi da  Koyon aikin gona ta jihar Bauchi da kuma babbar Kwalejin Kimiyya, fasaha da kere-kere mallakin gwamantin jihar Bauchi, ATAP.

Kazalika, kwamitin ya yi kira da a gaggauta dawo da aiwatar da tsarin karin girma na shekara-shekara ga wadanda suka dace da aka dakatar da yi ba tare da an bayyana a hukumance dalilin dakatarwar ba tun lokacin da gwamnati mai ci ta hau kan mulki.

Shugaban kungiyar ya ce kwamitin nasu ya nuna adawarsa kan shigar da ma’aikata tsarin taimakekeniya ta fansho duk kuwa da cewa hatta ma’aikatan Gwamnatin tarayya ma na kaurace wa tsarin domin wahalar da ke janyo wa ma’aikatan.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

A cewarsa, su na kuma da bukatar a dauki dukkanin matakan da suka dace wajen samar wa mambobin kungiyar rayuwa mai inganci da kuma tsaron hakkokinsu a kowani lokaci domin samun dama da sararin gudanar da aiki ba tare da wani fargaba ko dar-dar ba.

Abdulkadir Mohammed ya ce sun kuma yi adawa da cire wani kaso daga cikin albashin ma’aikatan da sunan shirin tallafin gidauniyar kiwon lafiya da ake kira BASHMA.

Mohammed ya ce bisa wadannan dalilai da sauran hakkokinsu da suke nema ne ya sanya suka zauna suka cimma matsayar tafiya yajin aikin gargadi, kodayake kafin wannan ya ce sun bai wa gwamantin wa’adi da jawo hankalinta tun da jimawa amma matsalolin nasu sai karuwa suke yi. Don haka ne suka ga dacewar tafiya yajin aikin.

Ya cigaba da cewa domin neman adalci dai, sun tuntubi hukumomin da abun ya shafa kan matsalolin nasu domin ganin an yi shawo kan kalubalen da suka hada da Akanta Janar na jihar, da kwamishinan ilimi, da sauran masu ruwa da tsaki kan lamarin amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba, duk da tilin wasikun da suka aike musu.

“Mun rubuta wasika muka aike wa mai girma gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad Abdulkadir a tunanin mu duk abun da suke faruwa bai ma san da su ba. Nan ma dai ba mu samu sauyi ko canji daga matsalolinmu ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Sanda Sun Damke ‘Yan Sane 6 a Jigawa

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mai Juna Biyu A Kaduna

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

11 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

12 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

15 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

18 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

20 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

21 hours ago
Next Post
Bauchi

'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mai Juna Biyu A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.