• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan ‘Yan Takarar Da Za Su Fafata A Zaben Gwamnan Jihar Kogi

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Manyan ‘Yan Takarar Da Za Su Fafata A Zaben Gwamnan Jihar Kogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta shirya tsaf domin gudanar da zaben gwamna a jihohin Kogi da Imo da kuma Bayelsa.

Za a gudanar da zabukan jihohin ne a ranar Asabar, 11 ga watan Nuwamban 2023.

  • Neja Za Ta Gyara Makarantun Rugagen Fulani
  • Gwamnonin PDP Sun Karyata Shirin Mubaya’a Ga Tinubu

A tsawon watanni bakwai da suka wuce, ‘yan takarar gwamna a jihar Kogi, na ta gudanar da yakin neman zabe a kokarin su na ganin sun kai ga nasara.

Yanzu haka akwai ‘yan takara 18 da ke takarar gwamnan a jihar ta Kogi.

‘Yan takarar za su fafata ne domin ganin wanda zai maye gurbin gwamna Yahaya Bello mai barin gado, wanda ke kammala wa’adin mulkinsa karo na biyu.

Labarai Masu Nasaba

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Jam’iyyar APC mai mulkin jihar na yin duk mai yiwuwa wajen ganin ta rike kujerar gwamnan yayin da jam’iyyun adawa kuma ke kokarin ganin sun kwace mulki daga hannun APC da ke kan mulki tsawon shekaru takwas.

Cikin jam’iyyu 18 da INEC ta tantance domin shiga zaben gwamna a jihar Kogi ya zuwa ranar 9 ga watan Nuwamban, 2023, ana ganin cewa shida ne kawai ke a kan gaba gabanin zaben na ranar Asabar.

Masana harkokin siyasa a jihar na ganin cewa fafatawar za ta fi zafi ne tsakanin jam’iyyu uku; APC, PDP, da kuma SDP.

Masanan sun kara da cewa manyan ‘yan takarar uku da ke sahun gaba a zaben sun fito ne daga kabilu daban-daban, kamar Ebira, Igala, da kuma Okun, kuma hakan zai iya yin tasiri sosai kan sakamakon zaben.

Sun ce yayin da jam’iyyar APC za ta iya samun yawan kuri’u daga tsakiyar jihar, SDP kuma za ta iya bayar da mamaki a gabashin jihar, inda ita kuma PDP mai dimbin magoya baya a yammacin jihar, za su zabi Dino Melaye.

Manyan ‘yan takarar guda uku da za su fafatawa a tsakaninsu su ne:

Sanata Dino Melaye – PDP

Sanata Dino Melaye shi ne mutumin da zai yi wa jam’iyyar PDP takara a zaben gwamnan Kogi a yau Asabar.

An haife shi ne a watan Janairun 1974 kuma dan siyasa ne mai yawan haifar da cece-kuce.

Tsohon Sanatan, ya yi karatun sakandare a Kwalejin Abdulaziz Attah, da ke Okene.

Daga nan ya tafi Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya a shekarar 2000 inda ya karanta ilimin Geography.

A shekara ta 2021, ya kammala karatu a Jami’ar Baze, inda ya karanta fannin Shari’a.

Melaye ya wakilci mazabar Kogi ta Yamma a majalisar dattawa daga 2015-2019.

Zamansa dan takarar jam’iyyar PDP, ya kara iza wutar adawa tsakaninsa da jam’iyyar APC a jihar.

Ana kuma ganin cewa dimbin magoya bayan jam’iyyar PDP na tare da shi, kuma suna shirye domin zaben shi a matsayin gwamnan jihar Kogi.

Ododo Ahmed Usman – APC

Ododo Usman shi ne dan takarar zaben gwamnan jihar Kogi a karkashin jam’iyyar APC a zaben da za a yi.

Usman-Ododo wanda dan kabilar Ebira ne da ya fito daga garin Okene, ya yi digirinsa na farko a fannin Akanta a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya.

Ya kuma yi digirinsa na biyu a fannin kasuwanci a Jami’ar Legas.

Kafin samun zama dan takarar gwamna a jam’iyyar APC, ya kasance babban mai binciken kudi na kananan hukumomin jihar, tsawon shekara bakwai da rabi, kuma an yi imanin cewa ya taka rawar gani a gwamnatin Yahaya Bello.

Murtala Yakubu Ajaka – SDP

Murtala Yakubu Ajaka ya kasance babban jigo a jam’iyyar APC a jihar Kogi, kafin komawarsa SDP.

Mista Ajaka ya fito ne daga karamar hukumar Igalamela, da ke gabashin jihar Kogi. Mazabar tana da yawan masu kada kuri’a.

Ya koma jam’iyyar SDP ne bayan kasa samun tikiti a APC, inda daga bisani ya samu nasarar zama dan takarar SDP a zaden gwamnan Kogi na 2023.

An yi imanin cewa dan takarar na SDP na iya samun kuri’u masu yawa a gabashin Kogi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCDino MelayeKogiOdodoPDPSDPZaben Gwamna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Neja Za Ta Gyara Makarantun Rugagen Fulani

Next Post

Bauchi Ta Mika Ragamar Filin Jirgin Tafawa Balewa Ga Tarayya

Related

An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

3 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

11 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

17 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

19 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

21 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

23 hours ago
Next Post
Filin Jirgin Tafawa

Bauchi Ta Mika Ragamar Filin Jirgin Tafawa Balewa Ga Tarayya

LABARAI MASU NASABA

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da ÆŠumi-É—umi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
ÆŠan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

ÆŠan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.