• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan ‘Yan Takarar Da Za Su Fafata A Zaben Gwamnan Jihar Kogi

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Manyan ‘Yan Takarar Da Za Su Fafata A Zaben Gwamnan Jihar Kogi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta shirya tsaf domin gudanar da zaben gwamna a jihohin Kogi da Imo da kuma Bayelsa.

Za a gudanar da zabukan jihohin ne a ranar Asabar, 11 ga watan Nuwamban 2023.

  • Neja Za Ta Gyara Makarantun Rugagen Fulani
  • Gwamnonin PDP Sun Karyata Shirin Mubaya’a Ga Tinubu

A tsawon watanni bakwai da suka wuce, ‘yan takarar gwamna a jihar Kogi, na ta gudanar da yakin neman zabe a kokarin su na ganin sun kai ga nasara.

Yanzu haka akwai ‘yan takara 18 da ke takarar gwamnan a jihar ta Kogi.

‘Yan takarar za su fafata ne domin ganin wanda zai maye gurbin gwamna Yahaya Bello mai barin gado, wanda ke kammala wa’adin mulkinsa karo na biyu.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Jam’iyyar APC mai mulkin jihar na yin duk mai yiwuwa wajen ganin ta rike kujerar gwamnan yayin da jam’iyyun adawa kuma ke kokarin ganin sun kwace mulki daga hannun APC da ke kan mulki tsawon shekaru takwas.

Cikin jam’iyyu 18 da INEC ta tantance domin shiga zaben gwamna a jihar Kogi ya zuwa ranar 9 ga watan Nuwamban, 2023, ana ganin cewa shida ne kawai ke a kan gaba gabanin zaben na ranar Asabar.

Masana harkokin siyasa a jihar na ganin cewa fafatawar za ta fi zafi ne tsakanin jam’iyyu uku; APC, PDP, da kuma SDP.

Masanan sun kara da cewa manyan ‘yan takarar uku da ke sahun gaba a zaben sun fito ne daga kabilu daban-daban, kamar Ebira, Igala, da kuma Okun, kuma hakan zai iya yin tasiri sosai kan sakamakon zaben.

Sun ce yayin da jam’iyyar APC za ta iya samun yawan kuri’u daga tsakiyar jihar, SDP kuma za ta iya bayar da mamaki a gabashin jihar, inda ita kuma PDP mai dimbin magoya baya a yammacin jihar, za su zabi Dino Melaye.

Manyan ‘yan takarar guda uku da za su fafatawa a tsakaninsu su ne:

Sanata Dino Melaye – PDP

Sanata Dino Melaye shi ne mutumin da zai yi wa jam’iyyar PDP takara a zaben gwamnan Kogi a yau Asabar.

An haife shi ne a watan Janairun 1974 kuma dan siyasa ne mai yawan haifar da cece-kuce.

Tsohon Sanatan, ya yi karatun sakandare a Kwalejin Abdulaziz Attah, da ke Okene.

Daga nan ya tafi Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya a shekarar 2000 inda ya karanta ilimin Geography.

A shekara ta 2021, ya kammala karatu a Jami’ar Baze, inda ya karanta fannin Shari’a.

Melaye ya wakilci mazabar Kogi ta Yamma a majalisar dattawa daga 2015-2019.

Zamansa dan takarar jam’iyyar PDP, ya kara iza wutar adawa tsakaninsa da jam’iyyar APC a jihar.

Ana kuma ganin cewa dimbin magoya bayan jam’iyyar PDP na tare da shi, kuma suna shirye domin zaben shi a matsayin gwamnan jihar Kogi.

Ododo Ahmed Usman – APC

Ododo Usman shi ne dan takarar zaben gwamnan jihar Kogi a karkashin jam’iyyar APC a zaben da za a yi.

Usman-Ododo wanda dan kabilar Ebira ne da ya fito daga garin Okene, ya yi digirinsa na farko a fannin Akanta a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya.

Ya kuma yi digirinsa na biyu a fannin kasuwanci a Jami’ar Legas.

Kafin samun zama dan takarar gwamna a jam’iyyar APC, ya kasance babban mai binciken kudi na kananan hukumomin jihar, tsawon shekara bakwai da rabi, kuma an yi imanin cewa ya taka rawar gani a gwamnatin Yahaya Bello.

Murtala Yakubu Ajaka – SDP

Murtala Yakubu Ajaka ya kasance babban jigo a jam’iyyar APC a jihar Kogi, kafin komawarsa SDP.

Mista Ajaka ya fito ne daga karamar hukumar Igalamela, da ke gabashin jihar Kogi. Mazabar tana da yawan masu kada kuri’a.

Ya koma jam’iyyar SDP ne bayan kasa samun tikiti a APC, inda daga bisani ya samu nasarar zama dan takarar SDP a zaden gwamnan Kogi na 2023.

An yi imanin cewa dan takarar na SDP na iya samun kuri’u masu yawa a gabashin Kogi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCDino MelayeKogiOdodoPDPSDPZaben Gwamna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Neja Za Ta Gyara Makarantun Rugagen Fulani

Next Post

Bauchi Ta Mika Ragamar Filin Jirgin Tafawa Balewa Ga Tarayya

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

16 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

20 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

22 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da É—umi-É—uminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

2 days ago
Next Post
Filin Jirgin Tafawa

Bauchi Ta Mika Ragamar Filin Jirgin Tafawa Balewa Ga Tarayya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.