ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Marubutan Da Akwai Hikima, Na Yanzu Sai Karyar Zuwa Waje – Amina

Ci gaba daga makon jiya

by Adamu Yusuf Indabo
3 years ago
Hikima

A karashen tattaunawar da wakilinmu, ADAMU YUSUF INDABO ya yi da marubuciyar yanar gizo, AMINA MA’AJI da muka fara kawo muku a makon jiya ta bambanta marubutan baya da na yanzu bisa fahimtarta, a karanta har karshe amar haka:

To daga 2015 da kika fara rubutu zuwa yau shekaru 8. Kin rubuta littattafai da adadinsu ya kai nawa?

Na rubuta littafi guda Goma Sha Biyu. Da suka hada da Namiji Krin Kunama, Ki Yi Min uzuri, Ni Da Haidar, A Kula Da Mu, Ashe Haka So Yake, Dan Adam Butulu, Aminatu, Halacci Ne, Gidan Marayu, Ina Mafita, ‘Yancin Mata, Zabi Biyu.

ADVERTISEMENT

To cikin su wanne ne bakandamiyar ki?

Gidan Marayu. Na sha wahala wajen rubuta littafin sannan ya samu karbuwan da ban yi zato ba. Ya jawo mun alkairi da yawa na samu kyau ta da yawa. Duk da ya fi ba ni wahala duk cikin littafan da na rubuta, dan na je gidan marayu kafun in samu ganin masu ruwa da tsaki a cikin gidan na sha wahala,  na sha kuka ganin yadda rayuwar marayu yake.

LABARAI MASU NASABA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

Cikin wanne yanayi da lokaci kika fi jin dadin yin rubutu?

Na fi jin dadin rubutu a lokacin da nake cikin farin ciki sannan ba ni da wata damuwa, ina son yin typing da dare yana sa in tsai da hankali na wajen yin rubutu a cikin nutsuwa.

To kuma ya batun kungiyoyin marubuta?

Na shiga kungiyoyi guda biyu rashin hadin kai ya sa na fita saboda yawanci ba ma kiyaye dokokin group shi ya sa yanzu bani da wani kungiya guda daya,  na shiga Haske da kuma perfect duk na fita Allah ya sa mu dace.

Kasancewar ki tsohuwar makaranciya ya za ki kwatanta marubutan da da kuma na yanzu ta fuskar kwarewa da kuma yin rubutu mai ma’ana?

Na ji dadin tambayar nan. Marubutanmu na da suna rubutu cikin hikima da basira ga labarin yana da ma’ana, sannan akwai darasi cikin sigar dabara sannan ba sa tsananta dogon labari. Na yanzu kuwa sai karyan ya tafi kasar waje a can za a yi rayuwa, alhalin marubuciyar ko nan da Sokoto ba ta je ba, amma za ki ji rubutun ya tafi. Kadan ne daga cikin su masu rubutu irin na da akwai wata marubuciya Badi’at Ibrahim, littafinta duk irin na da ne akwai hikima wajen rubuta shi. Sannan marubutan da ba su da mu da ka’idojin rubutu da yawa ba, na yanzu sukan yi amfani da ka’idojin rubutu. Misali kamar ni da Sadnaf Badi’at mukan rubuta ‘true life story’ ne dan gaskiya in ka ce in rubuta abun da bai faru da gaske ba shirme zan yi. Nakan yi bincike gidaje da yawa masu shigen irin labarin akwai littafi na Halacci ne littafin ya yi duba ga ‘yan shaye-shaye, na sha wahala sai da na je gun yan shaye-shaye cikin hikima tare da siya musu abinci da ruwa da lemo kafin na samu karin haske. Yana da kyau mu marubuta mu dinga yin bincike sosai kafin mu dora alkalaminmu. Allah ya yi mana jagora. Sannan ya kamata mu dinga rubuta labari a cikin jahar mu dan a gane a ina muke.

To daga fara rubutunki zuwa yau. Wadanne nasarori kika cimma ta silar rubutu?

Nasaran farko sanin manyan marubuta na biyu karban award guda daya na uku marubuta sun san ni.

To wanne irin kalubale kika hadu da shi?

Kalubalin da na fuskanta a cikin gida ne, Sam ba sa son in dinga rubutu a nasu fahimtar bata lokaci ne, sai daga baya suka gane rubutu hanya ce na isar da sako cikin hikima. Na biyu rashin hadin kan marubuta shi ke sani damuwa nakan dauki marubuta tamkar jinina amma rashin hadin kai shike damu na, hakika ba ni da kamar marubuci a rayuwata a duk in da marubuci yake ina alfahari da shi koda yau ne ya fara rubuta kalman ‘A’ a matsayin rubutu amma kash abun sai a hankali.

To mece ce shawararki na ganin an dinke wannan baraka ta rashin hadin kan marubuta?

Abu ne wanda za mu ce Allah ya hada kanmu kawai, dan gaskiya sai mun cire hassada kafun haduwar kai zai yi tasiri, mu cire kyashi ga junanmu, mu dauki rubutu a matsayin sana’a.

Wanna buri kike da shi a rayuwa?

Ina son in zama babbar marubuciyar da duk duniya a san ni koda a jahata ne na ci nasara sosai. Burina na biyu ina so mu yi gangamin hada taron marubutan online na kowani jaha a san juna.

A karshe wanna kira za ki yi ga ‘yan uwanki marubuta?

Ina kira ga marubuta yan uwana mu hada kanmu wajen gina gaskiya, sannan kananan marubuta musamman wanda ba su yi aure ba, su daina sako harkan da ta shafi gidan aure baranta na takai ga shimfida, ta kiyaye wannan su tsarkake alkalaminsu, su yi rubutu mai tsafta su ji tsoron Allah, dan in sun yi rubutu cikin rashin hankali zabsu karanta ranan da babu musu.

Wanna sako kike da shi ga masoyanki dake bibiyar dukkan rubuce-rubucenki?

Masoyana a koda yaushe ina alfahari da su. Kuma ni ma ina kaunarku masoyana.

Hikima
Adamu Yusuf Indabo
+ postsBio
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    An Yi Yekuwar Daukar Matakin Gaggawa Kan Take ‘Yancin ‘Yan Jarida
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Marubutan Batsa Ku Ji Tsoron Allah -Emili
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Ba Nanaye Ko Rashin Da’a Nake Rubutawa Ba – A.S Aikawa
  • Adamu Yusuf Indabo
    https://hausa.leadership.ng/author/adamu-yusuf-indabo/
    Marubuta Tamkar Madubi Suke Ga Al’ummah – Zainab Salihu Yarima

MASU ALAKA

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Zambar Kudi: Kotu Ta Tasa Keyar Dillalin Gidaje Zuwa Gidan Kaso
Adabi

EFCC Ta Kama Mutum 11 Masu Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba A Kwara

February 6, 2026
CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki
Adabi

CGI Babandede Mai Ritaya A Mizanin Kyawawan Halaye Da Kwazon Aiki

January 30, 2026
Next Post
Shari’ar Zaben Kano: Alhaki Kwikwiyo

Shari'ar Zaben Kano: Alhaki Kwikwiyo

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.