ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masallacin Zariya: Adadin Wadanda Suka Mutu Ya Kai 12

by Sadiq
2 years ago
Zariya

Adadin wadanda suka mutu sakamakon rushewar babban masallacin Zariya, a yammacin ranar Juma’a a garin Zariya na jihar Kaduna, ya kai 12.

Idan za a tuna cewa lamarin ya afku ne a daidai lokacin da masallata suke gudanar da sallar la’asar da misalin karfe 4 na yammacin ranar Juma’a.

  • Tsohon Gwamnan Kwara A Mulkin Soja, Latinwo Ya Kwanta Dama
  • Australia Ta Doke Faransa A Bugun Fanareti Inda Ta Kai Zagayen Kusa Da Na Karshe

A halin yanzu, gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, kakakin majalisar wakilai, Hon. Tajudeen Abbas, da kungiyar Jama’atul Nasir Islam (JNI), sun mika ta’aziyyarsu ga masarautar Zazzau da iyalan wadanda suka rasu.

ADVERTISEMENT

Gwamna Uba Sani, a cikin ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda abin ya shafa, ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka mutu.

Gwamnan ya gode wa Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli, bisa irin rawar da ya taka wajen hada kan al’ummarsa domin gudanar da aikin ceto, da bayar da taimako ga wadanda suka jikkata da kuma jajanta wa iyalan wadanda abin ya shafa.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Gwamnan ya kuma yaba da kokarin wadanda suka fara yin ceto, da ma’aikatan lafiya, da kuma nagari mutanen Zariya wajen ceto wadanda suka tsira.

Ya kuma bukaci al’ummar jihar da su yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu, ya kuma kara da cewa tuni tawagar manyan jami’an gwamnati karkashin jagorancin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Balarabe Abbas Lawal, ta isa Zariya don tantance halin da ake ciki.

“Gwamnatin jihar za ta kuma bayar da umarnin gudanar da bincike kan musabbabin faruwar lamarin,” in ji shi.

“Ina matukar bakin ciki da abin da ya faru a babban masallacin Zariya da ke jihar Kaduna, zuciyata na mika sakon ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da wadanda suka jikkata sakamakon rushewar masallacin Zariya.

“Ina kuma mika ta’aziyyata ga Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli, da daukacin al’ummar musulmi bisa wannan rashi. Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta wa wadanda suka rasu.

“Gwamnatin jihar Kaduna za ta taimaka wa wadanda wannan lamari ya rutsa da su,” in ji shi.

Har ila yau, babban sakataren JNI, Farfesa Khalid Abubakar Aliyu, a wata sanarwa da ya fitar ya yi kira ga hukumomi da su gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin aukuwar wannan mummunan lamari.

Hakazalika, a sakon ta’aziyyarsa, Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Abbass, ya bayyana wannan mummunan lamari a matsayin abin takaici da ban tausayi.

A wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Musa Abdullahi Krishi ya rabawa manema labarai, shugaban majalisar ya ce “zuciyarsa na alhinin faruwar lamarin, inda ya ce wannan shi ne labari mai ratsa zuciya da ya samu a ‘yan kwanakin nan.

Abbas, wanda ya bayyana alhininsa, ya kuma yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Next Post
Nijar: Ba A Kone Ofishin Jakadancin Nijeriya Ba – Jakada

Nijar: Ba A Kone Ofishin Jakadancin Nijeriya Ba - Jakada

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.