• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masallacin Zariya: Adadin Wadanda Suka Mutu Ya Kai 12

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Masallacin Zariya: Adadin Wadanda Suka Mutu Ya Kai 12
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Adadin wadanda suka mutu sakamakon rushewar babban masallacin Zariya, a yammacin ranar Juma’a a garin Zariya na jihar Kaduna, ya kai 12.

Idan za a tuna cewa lamarin ya afku ne a daidai lokacin da masallata suke gudanar da sallar la’asar da misalin karfe 4 na yammacin ranar Juma’a.

  • Tsohon Gwamnan Kwara A Mulkin Soja, Latinwo Ya Kwanta Dama
  • Australia Ta Doke Faransa A Bugun Fanareti Inda Ta Kai Zagayen Kusa Da Na Karshe

A halin yanzu, gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, kakakin majalisar wakilai, Hon. Tajudeen Abbas, da kungiyar Jama’atul Nasir Islam (JNI), sun mika ta’aziyyarsu ga masarautar Zazzau da iyalan wadanda suka rasu.

Gwamna Uba Sani, a cikin ta’aziyyarsa ga iyalan wadanda abin ya shafa, ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka mutu.

Gwamnan ya gode wa Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli, bisa irin rawar da ya taka wajen hada kan al’ummarsa domin gudanar da aikin ceto, da bayar da taimako ga wadanda suka jikkata da kuma jajanta wa iyalan wadanda abin ya shafa.

Labarai Masu Nasaba

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Gwamnan ya kuma yaba da kokarin wadanda suka fara yin ceto, da ma’aikatan lafiya, da kuma nagari mutanen Zariya wajen ceto wadanda suka tsira.

Ya kuma bukaci al’ummar jihar da su yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu, ya kuma kara da cewa tuni tawagar manyan jami’an gwamnati karkashin jagorancin sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Balarabe Abbas Lawal, ta isa Zariya don tantance halin da ake ciki.

“Gwamnatin jihar za ta kuma bayar da umarnin gudanar da bincike kan musabbabin faruwar lamarin,” in ji shi.

“Ina matukar bakin ciki da abin da ya faru a babban masallacin Zariya da ke jihar Kaduna, zuciyata na mika sakon ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da wadanda suka jikkata sakamakon rushewar masallacin Zariya.

“Ina kuma mika ta’aziyyata ga Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli, da daukacin al’ummar musulmi bisa wannan rashi. Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta wa wadanda suka rasu.

“Gwamnatin jihar Kaduna za ta taimaka wa wadanda wannan lamari ya rutsa da su,” in ji shi.

Har ila yau, babban sakataren JNI, Farfesa Khalid Abubakar Aliyu, a wata sanarwa da ya fitar ya yi kira ga hukumomi da su gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin aukuwar wannan mummunan lamari.

Hakazalika, a sakon ta’aziyyarsa, Kakakin Majalisar Wakilai, Hon. Abbass, ya bayyana wannan mummunan lamari a matsayin abin takaici da ban tausayi.

A wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Musa Abdullahi Krishi ya rabawa manema labarai, shugaban majalisar ya ce “zuciyarsa na alhinin faruwar lamarin, inda ya ce wannan shi ne labari mai ratsa zuciya da ya samu a ‘yan kwanakin nan.

Abbas, wanda ya bayyana alhininsa, ya kuma yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JikkataKadunaRasuwaRushewar MasallaciZariya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsohon Gwamnan Kwara A Mulkin Soja, Latinwo Ya Kwanta Dama

Next Post

Nijar: Ba A Kone Ofishin Jakadancin Nijeriya Ba – Jakada

Related

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya
Labarai

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

4 hours ago
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

5 hours ago
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

7 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

8 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

9 hours ago
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

11 hours ago
Next Post
Nijar: Ba A Kone Ofishin Jakadancin Nijeriya Ba – Jakada

Nijar: Ba A Kone Ofishin Jakadancin Nijeriya Ba - Jakada

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga Kwaɗayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.