• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Yi Martani Kan Tuhume-Tuhumen Da Ake Yi Wa Alhassan Ado Doguwa

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
An Kama Alhassan Doguwa Kan Zargin Kisan Kai A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansanda ta Jihar Kano ta gurfanar da shugaban masu rinjaye na majalisar wakilan kasar Alhassan Ado Doguwa a gaban kotun majistire ta jihar, bisa tuhumar sa da hannu a tarzomar zabe, inda wasu mutane uku suka rasa rayukansu a yankin mazabarsa.

Mallaka da amfani da makami babu izini, tsarawa da hada baki wajen aikata miyagun laifuka, kisan kai da kuma tada hankalin jama’a, suna daga cikin abubuwan da aka tuhumi Alhassan Ado Doguwa a zauren kotun.

  • Buhari Zai Kaddamar Da Aiki Sannan Ya Gana Da ‘Yan Kasuwar ‘Monday Market’ A Borno 
  • Peter Obi Da Jam’iyyarsa Ta Labour Sun Ce Su Ne Suka Yi Nasara A Zaben Shugaban Kasa Ba Tunibu Ba

Lauya mai gabatar da kara Barrister A’isha Salisu, tace rahotan farko na binciken ‘yan sanda ya nuna akwai zargi akan Alhassan Ado Doguwa, na cewa ya hada baki da wani mai suna Bashir Dahiru na kauyen Jammaje, da Bala mai Doki, da Hamisu Musa, da Nazifi Asananic, da Abdullahi Haruna, da kuma karin wasu da dama da yanzu haka ‘yan sanda ke nema ruwa a jallo bayan da aka ce sun tada fitina ta hanyar cinna wuta a sakatariyar NNPP ta karamar hukumar Tudunwada ta yankin kudancin Kano.

Kazalika, ana tuhumar Alhassan Ado Doguwa da raunata wani mai suna Alhassan Muhammad Sarkin Fawa da wasu mutane da dama, kana ya harbi wani Ibrahim Danbala, bayan haka ya jikkata wani Auwal Dauda ya kuma raunata wasu mutane da wuka.

Tun da fari dai Alhassan Ado Doguwa ya fada wa kotu cewa, yana muradin a karanto masa tuhume-tuhumen da harshen Hausa zalla maimakon yaren turanci, bukatar da kotun ta amince da ita nan take.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Daga bisani dai lauyan Alhassan Ado Doguwa Barr Abdul Adamu, ya roki kotun ta bashi belinsa, la’akari da matsayinsa a majalisar wakilan Najeriya, amma Barr Aisha Salisu ta soki yunkurin bada belin.

Alkalin kotun mai shari’a Ibrahim Mansur Yola, ya bada umurnin a tsare Alhassan Ado Doguwa a gidan Kurkuku. Yana mai cewa la’akari da girman laifukan da ake tuhumar dan majalisar tarayyar, kotunsa ba ta da hurumin yin shari’ar, amma ya dage sauraron shari’ar zuwa ranar 7 ga wannan wata na Maris, kuma ana sa ran gabanin lokacin an sami karin bayanai da shawarwari daga ma’aikatar shari’a ta jihar Kano.

Yanzu haka dai masana a fannoni dabamdaban na tsokaci akan wannan batu.

Dokta Sa’idu Ahmad Dukawa, masanin kimiyyar siyasa a Jami’ar Bayero da ke Kano, ya ce matakin ya fara nuna cewa ‘yan sanda sun fara yin aikin su yadda ya kamata kuma hakan zai zama darasi ga ‘yan siyasar da ke sha’awar yin abin da ake zargin shi Alhassan Ado Doguwa da aikatawa.

Shi kuwa lauyan kare hakkin bil’adama Audu Bulama Bukarti, cewa yayi abin da ‘yansandan suka yi na gurfanar da wanda ake tuhuma a gaban kotu yana da kyau, amma sai bayan an tabbatar da hukuncin daya dace akansa bayan an tabbatar da laifi, san nan ne za a yaba wa ‘yansanda da alkalai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaAlhassan Ado DoguwaDoguwaKisaKotuTudun wadaZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Zai Kaddamar Da Aiki Sannan Ya Gana Da ‘Yan Kasuwar ‘Monday Market’ A Borno 

Next Post

Atiku Zai Yi Jawabi Da Yamma Kan Faduwa Zaben Shugaban Kasa

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

12 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

21 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

23 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

24 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Atiku Zai Yi Jawabi Da Yamma Kan Faduwa Zaben Shugaban Kasa

Atiku Zai Yi Jawabi Da Yamma Kan Faduwa Zaben Shugaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.