• English
  • Business News
Wednesday, July 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masana Sun Yi Martani Kan Tuhume-Tuhumen Da Ake Yi Wa Alhassan Ado Doguwa

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
An Kama Alhassan Doguwa Kan Zargin Kisan Kai A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansanda ta Jihar Kano ta gurfanar da shugaban masu rinjaye na majalisar wakilan kasar Alhassan Ado Doguwa a gaban kotun majistire ta jihar, bisa tuhumar sa da hannu a tarzomar zabe, inda wasu mutane uku suka rasa rayukansu a yankin mazabarsa.

Mallaka da amfani da makami babu izini, tsarawa da hada baki wajen aikata miyagun laifuka, kisan kai da kuma tada hankalin jama’a, suna daga cikin abubuwan da aka tuhumi Alhassan Ado Doguwa a zauren kotun.

  • Buhari Zai Kaddamar Da Aiki Sannan Ya Gana Da ‘Yan Kasuwar ‘Monday Market’ A Borno 
  • Peter Obi Da Jam’iyyarsa Ta Labour Sun Ce Su Ne Suka Yi Nasara A Zaben Shugaban Kasa Ba Tunibu Ba

Lauya mai gabatar da kara Barrister A’isha Salisu, tace rahotan farko na binciken ‘yan sanda ya nuna akwai zargi akan Alhassan Ado Doguwa, na cewa ya hada baki da wani mai suna Bashir Dahiru na kauyen Jammaje, da Bala mai Doki, da Hamisu Musa, da Nazifi Asananic, da Abdullahi Haruna, da kuma karin wasu da dama da yanzu haka ‘yan sanda ke nema ruwa a jallo bayan da aka ce sun tada fitina ta hanyar cinna wuta a sakatariyar NNPP ta karamar hukumar Tudunwada ta yankin kudancin Kano.

Kazalika, ana tuhumar Alhassan Ado Doguwa da raunata wani mai suna Alhassan Muhammad Sarkin Fawa da wasu mutane da dama, kana ya harbi wani Ibrahim Danbala, bayan haka ya jikkata wani Auwal Dauda ya kuma raunata wasu mutane da wuka.

Tun da fari dai Alhassan Ado Doguwa ya fada wa kotu cewa, yana muradin a karanto masa tuhume-tuhumen da harshen Hausa zalla maimakon yaren turanci, bukatar da kotun ta amince da ita nan take.

Labarai Masu Nasaba

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

Daga bisani dai lauyan Alhassan Ado Doguwa Barr Abdul Adamu, ya roki kotun ta bashi belinsa, la’akari da matsayinsa a majalisar wakilan Najeriya, amma Barr Aisha Salisu ta soki yunkurin bada belin.

Alkalin kotun mai shari’a Ibrahim Mansur Yola, ya bada umurnin a tsare Alhassan Ado Doguwa a gidan Kurkuku. Yana mai cewa la’akari da girman laifukan da ake tuhumar dan majalisar tarayyar, kotunsa ba ta da hurumin yin shari’ar, amma ya dage sauraron shari’ar zuwa ranar 7 ga wannan wata na Maris, kuma ana sa ran gabanin lokacin an sami karin bayanai da shawarwari daga ma’aikatar shari’a ta jihar Kano.

Yanzu haka dai masana a fannoni dabamdaban na tsokaci akan wannan batu.

Dokta Sa’idu Ahmad Dukawa, masanin kimiyyar siyasa a Jami’ar Bayero da ke Kano, ya ce matakin ya fara nuna cewa ‘yan sanda sun fara yin aikin su yadda ya kamata kuma hakan zai zama darasi ga ‘yan siyasar da ke sha’awar yin abin da ake zargin shi Alhassan Ado Doguwa da aikatawa.

Shi kuwa lauyan kare hakkin bil’adama Audu Bulama Bukarti, cewa yayi abin da ‘yansandan suka yi na gurfanar da wanda ake tuhuma a gaban kotu yana da kyau, amma sai bayan an tabbatar da hukuncin daya dace akansa bayan an tabbatar da laifi, san nan ne za a yaba wa ‘yansanda da alkalai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaAlhassan Ado DoguwaDoguwaKisaKotuTudun wadaZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Zai Kaddamar Da Aiki Sannan Ya Gana Da ‘Yan Kasuwar ‘Monday Market’ A Borno 

Next Post

Atiku Zai Yi Jawabi Da Yamma Kan Faduwa Zaben Shugaban Kasa

Related

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura
Manyan Labarai

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

10 hours ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

11 hours ago
Tinubu Ya Isa Katsina Don Tarbar Gawar Buhari
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Katsina Don Tarbar Gawar Buhari

11 hours ago
Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura
Manyan Labarai

Buhari Na Cikin Ƙoshin Lafiya Kwana Ɗaya Kafin Rasuwarsa – Mamman Daura

11 hours ago
Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina
Manyan Labarai

Buhari Da Ya Daɗe Da Rasuwa Idan A Asibitocin Nijeriya Ake Duba Shi – Adesina

13 hours ago
HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura
Hotuna

HOTUNA: An Tsaurara Tsaro A Gidan Buhari Da Ke Daura

14 hours ago
Next Post
Atiku Zai Yi Jawabi Da Yamma Kan Faduwa Zaben Shugaban Kasa

Atiku Zai Yi Jawabi Da Yamma Kan Faduwa Zaben Shugaban Kasa

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

July 15, 2025
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 15, 2025
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

July 15, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.