• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mastalar Tsaro: Jihohi Sun Kashe Naira Biliyan 214 Wajen Sayen Makamai

by Yusuf Shuaibu
1 month ago
in Labarai
0
Mastalar Tsaro: Jihohi Sun Kashe Naira Biliyan 214 Wajen Sayen Makamai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jihohi talatin da biyar sun kashe naira biliyan 214 wajen kula da jami’an tsaron sa-kai, shirye-shiryen tsaro, da sayen makamai da kayan aiki a cikin kasafin kudinsu na 2025, kamar yadda jaridar The Punch ta ruwaito.

Duk da dimbin kudaden da aka ware don magance rashin tsaro, akalla mutane 367 aka kashe a lokacin bikin sabuwar shekara da bikin Sallah tsakanin 2019 zuwa 2025.

  • Sojoji Sun Lalata Matatun Mai 20 A Yankin Niger Delta
  • Rundunar PLA Ta Kasar Sin Ta Kammala Atisayen Hadin Gwiwa Na Kwanan Nan

Kasafin kudin jihohi yana cikin shafin BudgIT na intanet wanda ke aiki a matsayin ma’ajiyar bayanan kasafin kudin gwamnati.

Babban kuri’ar, wanda aka yi niyyar gudanarwa don karfafa tsaro a duk fadin kasar nan, ya haifar da damuwa game da ingancin wadannan matakan, yayin da ‘yan kasa ke ci gaba da fuskantar tashin hankali.

Duk da cewa alhakkin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi ya kasance a hannun gwamnatin tarayya, karuwar garkuwa da mutane, fashi da makami da sauran nau’ikan tashin hankali ya tilasta wa gwamnonin jihohi da yawa kafa nasu dabarun tsaro na cikin gida don yaki da barazanar tsaro.

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Duk da wadannan kokari, amma har yau su haifar da sakamakon da ake bukata ba, yayin da masu aikata laifuka ke ci gaba da aikata ta’addanci ba tare da a hukunta su ba, suna ci gaba da ta’addanci a kan ‘yan kasa.

A watan da ya gabata, an ruwaito cewa an kashe mutane 30 a hare-haren da aka kai a jihohin Ondo, Benuwai, da Nasarawa, wadanda lamarin ya shafa suka yi kira ga gwamnati ta dauki matakin gaggawa.

Rahotanni sun ce an sace masu bincike tara a Ondo, yayin da aka sace mazauna gari biyu, wasu hudu kuma sun samu raunukan bindiga da adduna a Edo.

A Benuwai, zanga-zangar tashin hankali ta varke a Naka, hedkwatar karamar hukumar Gwer ta Yamma, bayan da wasu ‘yan ta’adda suka yi wa jami’an tsaron sa-kai uku kwanton bauna kuma suka kashe su.

A Jihar Nasarawa kuwa, rikicin al’umma a garin Farin Dutse ya rikide zuwa tashin hankali, inda ya yi sanadiyyar mutuwar akalla mutane bakwai, ciki har da wata mata mai juna biyu.

A makon da ya gabata, an kashe mutane 16 da ake kyautata zaton mafarauta ne a Uromi na Jihar Edo. Lamarin ya haifar da cece-kuce a fadin kasar nan, musamman ma a arewa.

Binciken ya nuna cewa a cikin watanni uku na farko na 2025, an samu lamarin garkuwa da mutane 2,819, tare da mutuwar mutane 3,190 da kuma jikkata 1,123. An dai samu lamarin ne a cikin kananan hukumomi 428 daga cikin 774.

Binciken kasafin kudin ya nuna cewa dukkan jihohin sun amince da sayen makamai da kayan tsaro.

Jihar Abiya ta ware naira miliyan 554.58 don sayen kayan tsaro da makamai, wanda ke nuna jajircewa na inganta tsarota.

Har ila yau, Jihar Adamawa ta ware makudan naira biliyan 3.82 don irin wannan dalili, wanda ke nuna kaso mai yawa a kasafin kudinta.

Akwa-Ibom ta bi sahu, inda ta ware naira biliyan 10.1 don sayen makamai da alburusai, jihar Edo ta ware naira miliyan 849, yayin da Anambra ta kashe naira biliyan 2.73 don bukatun tsaro.

Sauran sun hada da Bauchi wacce ta ware naira miliyan 889.71, yayin da Bayelsa ta ware naira biliyan 10.187.

Kasafin kudin tsaro na Benuwai ya kai naira biliyan 1.46, yayin da Ekiti da Kuros Ribas suka ware naira miliya 30 da naira miliya 10 bi da bi.

Kasafin kudin Borno na tsaro ya kai naira biliyan 1.92, yayin da Delta ta ware naira biliyan 2.84. Inugu na daya daga cikin mafi girman kaso a kudu maso gabas, ta ware naira biliyan 11.41.

Haka kuma Jihar Gombe ta ware naira miliyan 725.05, don sayen kayan tsaro da kuma tallafa wa ayyukan ma’aikatar tsaron jihar.

A Imo kuwa, Gwamna Hope Uzodinma ya ware naira miliyan 820.42 ga ma’aikatar tsaron cikin gida da kungiyoyin sa-kai. Jigawa da Kaduna sun ware naira miliyan 40 da naira miliyan 40.74 bi da bi.

Jihohin Kano, Katsina, da Kebbi suma sun ba da fifiko ga tsaro, inda Kano ta ware naira biliyan 1.42, Katsina naira biliyan 5.28, Kebbi mafi girma a tsakanin jihohin arewa na naira biliyan 21.81.

Rabon Kogi ya kai naira biliyan 11.06, yayin da Kwara ta ware naira miliyan 37 don ayyukan tsaro.

A kudu maso yamma, Jihar Ogun ta tanadi naira biliyan 4.81 don tsaro.

Amotekun, kungiyar tsaron yankin kotu, ta karbi kaso girma na naira biliyan 1.79, yayin da Safe-Corps kuma ta samu naira miliyan 459.62.

A gefe guda, Jihar Ondo ta kashe naira biliyan 7.07, tare da Naira biliyan 7.06 zuwa ga Amotekun. Jihohin Osun da Oyo sun ware naira biliyan 1.525 da naira biliyan 4.88 bi da bi, don tsaro.

An kiyasta kasafin kudin tsaro na Filato a kan naira biliyan 7.36, yayin da Jihar Ribas ta ware mafi girman kaso don tsaro a shekarar 2025, na naira biliyan 39.82 da aka ware don kayan tsaro.

Kasafin kudin tsaro na Sakkwato ya kai naira biliyan 10.57, Taraba ta ware naira biliyan 4.15, Yobe ta ware naira miliya 50, Zamfara ta ware naira biliyan 32.29.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JihohiKudi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bruno Fernandes Ba Na Sayarwa Ba Ne – Ruben Amorim

Next Post

Bude Kofa Da Hadin Gwiwa Da Juna Kalmomi Ne Mafi Dadi

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

2 hours ago
Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

4 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

5 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

6 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

7 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

8 hours ago
Next Post
Bude Kofa Da Hadin Gwiwa Da Juna Kalmomi Ne Mafi Dadi

Bude Kofa Da Hadin Gwiwa Da Juna Kalmomi Ne Mafi Dadi

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.