ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mastalar Tsaro: Jihohi Sun Kashe Naira Biliyan 214 Wajen Sayen Makamai

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Jihohi

Jihohi talatin da biyar sun kashe naira biliyan 214 wajen kula da jami’an tsaron sa-kai, shirye-shiryen tsaro, da sayen makamai da kayan aiki a cikin kasafin kudinsu na 2025, kamar yadda jaridar The Punch ta ruwaito.

Duk da dimbin kudaden da aka ware don magance rashin tsaro, akalla mutane 367 aka kashe a lokacin bikin sabuwar shekara da bikin Sallah tsakanin 2019 zuwa 2025.

  • Sojoji Sun Lalata Matatun Mai 20 A Yankin Niger Delta
  • Rundunar PLA Ta Kasar Sin Ta Kammala Atisayen Hadin Gwiwa Na Kwanan Nan

Kasafin kudin jihohi yana cikin shafin BudgIT na intanet wanda ke aiki a matsayin ma’ajiyar bayanan kasafin kudin gwamnati.

ADVERTISEMENT

Babban kuri’ar, wanda aka yi niyyar gudanarwa don karfafa tsaro a duk fadin kasar nan, ya haifar da damuwa game da ingancin wadannan matakan, yayin da ‘yan kasa ke ci gaba da fuskantar tashin hankali.

Duk da cewa alhakkin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi ya kasance a hannun gwamnatin tarayya, karuwar garkuwa da mutane, fashi da makami da sauran nau’ikan tashin hankali ya tilasta wa gwamnonin jihohi da yawa kafa nasu dabarun tsaro na cikin gida don yaki da barazanar tsaro.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Duk da wadannan kokari, amma har yau su haifar da sakamakon da ake bukata ba, yayin da masu aikata laifuka ke ci gaba da aikata ta’addanci ba tare da a hukunta su ba, suna ci gaba da ta’addanci a kan ‘yan kasa.

A watan da ya gabata, an ruwaito cewa an kashe mutane 30 a hare-haren da aka kai a jihohin Ondo, Benuwai, da Nasarawa, wadanda lamarin ya shafa suka yi kira ga gwamnati ta dauki matakin gaggawa.

Rahotanni sun ce an sace masu bincike tara a Ondo, yayin da aka sace mazauna gari biyu, wasu hudu kuma sun samu raunukan bindiga da adduna a Edo.

A Benuwai, zanga-zangar tashin hankali ta varke a Naka, hedkwatar karamar hukumar Gwer ta Yamma, bayan da wasu ‘yan ta’adda suka yi wa jami’an tsaron sa-kai uku kwanton bauna kuma suka kashe su.

A Jihar Nasarawa kuwa, rikicin al’umma a garin Farin Dutse ya rikide zuwa tashin hankali, inda ya yi sanadiyyar mutuwar akalla mutane bakwai, ciki har da wata mata mai juna biyu.

A makon da ya gabata, an kashe mutane 16 da ake kyautata zaton mafarauta ne a Uromi na Jihar Edo. Lamarin ya haifar da cece-kuce a fadin kasar nan, musamman ma a arewa.

Binciken ya nuna cewa a cikin watanni uku na farko na 2025, an samu lamarin garkuwa da mutane 2,819, tare da mutuwar mutane 3,190 da kuma jikkata 1,123. An dai samu lamarin ne a cikin kananan hukumomi 428 daga cikin 774.

Binciken kasafin kudin ya nuna cewa dukkan jihohin sun amince da sayen makamai da kayan tsaro.

Jihar Abiya ta ware naira miliyan 554.58 don sayen kayan tsaro da makamai, wanda ke nuna jajircewa na inganta tsarota.

Har ila yau, Jihar Adamawa ta ware makudan naira biliyan 3.82 don irin wannan dalili, wanda ke nuna kaso mai yawa a kasafin kudinta.

Akwa-Ibom ta bi sahu, inda ta ware naira biliyan 10.1 don sayen makamai da alburusai, jihar Edo ta ware naira miliyan 849, yayin da Anambra ta kashe naira biliyan 2.73 don bukatun tsaro.

Sauran sun hada da Bauchi wacce ta ware naira miliyan 889.71, yayin da Bayelsa ta ware naira biliyan 10.187.

Kasafin kudin tsaro na Benuwai ya kai naira biliyan 1.46, yayin da Ekiti da Kuros Ribas suka ware naira miliya 30 da naira miliya 10 bi da bi.

Kasafin kudin Borno na tsaro ya kai naira biliyan 1.92, yayin da Delta ta ware naira biliyan 2.84. Inugu na daya daga cikin mafi girman kaso a kudu maso gabas, ta ware naira biliyan 11.41.

Haka kuma Jihar Gombe ta ware naira miliyan 725.05, don sayen kayan tsaro da kuma tallafa wa ayyukan ma’aikatar tsaron jihar.

A Imo kuwa, Gwamna Hope Uzodinma ya ware naira miliyan 820.42 ga ma’aikatar tsaron cikin gida da kungiyoyin sa-kai. Jigawa da Kaduna sun ware naira miliyan 40 da naira miliyan 40.74 bi da bi.

Jihohin Kano, Katsina, da Kebbi suma sun ba da fifiko ga tsaro, inda Kano ta ware naira biliyan 1.42, Katsina naira biliyan 5.28, Kebbi mafi girma a tsakanin jihohin arewa na naira biliyan 21.81.

Rabon Kogi ya kai naira biliyan 11.06, yayin da Kwara ta ware naira miliyan 37 don ayyukan tsaro.

A kudu maso yamma, Jihar Ogun ta tanadi naira biliyan 4.81 don tsaro.

Amotekun, kungiyar tsaron yankin kotu, ta karbi kaso girma na naira biliyan 1.79, yayin da Safe-Corps kuma ta samu naira miliyan 459.62.

A gefe guda, Jihar Ondo ta kashe naira biliyan 7.07, tare da Naira biliyan 7.06 zuwa ga Amotekun. Jihohin Osun da Oyo sun ware naira biliyan 1.525 da naira biliyan 4.88 bi da bi, don tsaro.

An kiyasta kasafin kudin tsaro na Filato a kan naira biliyan 7.36, yayin da Jihar Ribas ta ware mafi girman kaso don tsaro a shekarar 2025, na naira biliyan 39.82 da aka ware don kayan tsaro.

Kasafin kudin tsaro na Sakkwato ya kai naira biliyan 10.57, Taraba ta ware naira biliyan 4.15, Yobe ta ware naira miliya 50, Zamfara ta ware naira biliyan 32.29.

Jihohi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Bude Kofa Da Hadin Gwiwa Da Juna Kalmomi Ne Mafi Dadi

Bude Kofa Da Hadin Gwiwa Da Juna Kalmomi Ne Mafi Dadi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.